ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Soki Zaben Kananan Hukumomi A Matsayin Cin Fuska Ga Dimokuradiyya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majalisa

Majalisar wakilai ta soki yadda gwamnatocin jihohi ke gudanar da zaben kananan hukumomi, inda ta bayyana shi a matsayin cin fuska ga dimokuradiyya.

A cewarsu, wannan lamari ya gurgunta ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi, kuma dole ne a magance lamarin domin a kiyaye ka’idojin dimokuradiyya.

  • Gwamnatin Kano Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Fadar Sarkin Kano 
  • Gwamnoni Sun Miƙa Ta’aziyya Ga Waɗanda Wani Abu Ya Fashe Da Su A Mota A Zamfara

Shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajuddeen ya bayyana hakan ne a jawabinsa na bude taron tattaunawa kan gyara zaben kananan hukumomi da tsarin mulki na kasa, wanda kwamitin majalisar kan duba kundin tsarin mulki ya shirya a ranar Litinin da ta gabata a Abuja.

ADVERTISEMENT

Tajuddeen ya ce, “Lokacin da zabubbuka suka kasance mara tsari, inda jam’iyya mai mulki ta mamaye dukkan mukamai, ya bayyana a fili muna cewa wanna cin fuska ne ga ka’idojin dimokuradiyya,” in ji Tajuddeen. Ya kara da cewa irin wadannan zabukan ba wai kawai na kawo cikas ga dimokuradiyya ba ne, har ma suna haifar da matukar damuwa game da daidaito da ayyukan kananan hukumomin.

“Wannan yanayin ba abin kunya ba ne kawai, yana kawo babbar barazana ga dimokuradiyyarmu. Yana haifar da mummunn yanayi, inda abubuwan da ba a so suke kutsawa cikin kananan hukumomi, galibi ba su da karfin da ake bukata da hangen nesa don gudanar da mulki yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Saboda haka, kananan hukumomi sun zama ‘yan amshin shatan gwamnatocin jihohi ko kuma ‘yan amshin shata a hannun ubangidan siyasa wadanda ke yin magudin zabe domin samun riban kashin kai,” in ji shi.

Tajuddeen ya bayyana rashin isassun kudade a matsayin daya daga cikin manyan kalubalen da kananan hukumomi ke fuskanta. “Yawancin gwamnatocin kananan hukumomi suna aiki da kasafin kudin da bai isa ya sauke nauyin da ke kansu ba,” in ji shi.

Ya kuma jaddada batun ‘yancin cin gashin kai, inda ya ce gwamnatocin jihohi ne ke sarrafa kananan hukumomi, wanda hakan ke haifar da tsoma baki wajen yanke shawara. A cewarsa, wannan rashin ‘yancin kai ne kuma yana dakushe romon dimokuradiyya a matakin kananan hukumomi.

Rashin isassun iya aiki daga fannin albarkatun Dan’adam da tsare-tsaren hukumomi ya kuma kawo cikas ga ingantaccen shugabanci a matakin kananan hukumomi. Yawancin ma’aikatan kananan hukumomi ba su da horo da kwarewa da ake bukata don gudanar da ingantaccen aiki, wanda hakan ke shafar samar da ayyuka da kuma sauke nauyin al’umma wajen gudanar da mulkin kananan hukumomi.

A halin da ake ciki, mataimakin shugban majalisar wakilai, Benjamin Okezie Kalu, wanda shi ne ya shugaban kwamitin majalisar kan yi wa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima, ya jaddada bukatar hada karfi da karfe a tsakanin masu ruwa da tsaki domin samun gyara mai ma’ana a harkokin kananan hukumomin Nijeriya.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Guguwa Mai Ƙarfi Ta Sa An Soke Wasan Liverpool Da Everton Na Yau

Guguwa Mai Ƙarfi Ta Sa An Soke Wasan Liverpool Da Everton Na Yau

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.