• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Tsaro
0
Majalisar Dinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dinkin Duniya ta shirya wani muhimmin taro na masu ruwa da tsaki a kan harkar tsaro, laifuffuka da shaye-shayen miyagun kwayoyi a Jihar Zamfara.

Taron, wanda aka fara shi Litinin da ta gabata a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau, ofishin kula da shaye-shayen miyagun kwayoyi da laifuffuka na Majalisar Dinkin Duniya da ke Nijeriya ne ya shirya shi.

  • Sanata Yari Ya Samar Da Taki Ga Manoman Zamfara A Kan Naira 20,000
  • NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

Mai magana da yawun Gwamnan Jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu a Gusau, ya bayyana cewa taron, wani shiri ne fayyacewa da lalubo hanyoyin mayar da martani game da matsalolin harkar tsaro da shaye-shayen miyagun kwayoyi.

Sulaiman Bala ya kara da cewa, wata tawagar Majalisar Dinkin Duniya karkashin jagorancin, Oliber Stolpe, wanda kuma shi ne wakili a Nijeriya na UNODC, taron zai tattaro masu ruwa da tsaki, inda za su zauna na tsawon kwanaki uku.

Sanarwar ta ce, “A wani muhimmin abu na masu ruwa da tsaki, ofishin kula da shaye-shayen miyagun kwayoyi da laifuffuka na Majalisar Dinkin Duniya (UNODC) ya shirya wani taron kara wa juna sani na kwana uku a kan harkar tsaro yau a Gusau.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

“Taron ya samar da masu ruwa da tsaki na cikin gida da wasu baki daga Majalisar Dinkin Duniya, inda za su yi zuzzurfan nazari domin samar da hanyoyin magance duk wani yanayi na tsaro, laifuffuka da shaye-shayen miyagun kwayoyi a Jihar Zamfara.

“Taron ya bayyana ingantattun ayyuka da kuma hanyoyin da za a bi daga ciki da wajen Nijeriya wajen tunkarar wadannan kalubale don samar da wani shiri na hadin gwiwa.”

A jawabinsa na bude taron, Gwamna Lawal ya jaddada cewa, kwakkwarar ta-waga ta masana daga Majalisar Dinkin Duniya sun nuna aniyarsu ta hadin gwiwa wajen magance kalubalen da ke addabar Zamfara da suka hada da ’yan bindiga da shaye-shayen miyagun kwayoyi.

Ya ce, “Kwanan nan na ziyarci Majalisar Dinkin Duniya domin neman shiga tsakani wajen magance wasu matsalolin da muke fuskanta, inda na samu kyakkyawar alaka da Amina J. Mohammed, mataimakiyar Sakatare Janar ta Majalisar Dinkin Duniya da kuma sauran bangarorin da take jagoranta ciki har da shugaban ofishin kula da miyagun kwayoyi da sauran laifuka.

“Saboda haka, wannan taron kara wa juna sani shaida ne na himmar da Majalisar Dinkin Duniya ke da shi na cika alkawuran da ta dauka don taimaka mana mu wajen kara fahimtar yadda za mu magance kalubalen da mu ke fuskanta. Muna matukar godiya.

“Sama da shekaru goma, Zamfara tana fama da wadannan matsalolin da ke kawo cikas ga tsaro da zaman lafiyar al’ummarmu da kuma kawo cikas ga ci gaban za-mantakewa da tattalin arziki. Don haka gwamnatina ta dauki wannan ziyara da taron bita da muhimmanci, domin sakamakon zai nuna yadda manufofinmu za su kasance wajen dabarun yaki da wadannan kalubale.

“Na yi farin cikin ganin cewa za a tattauna batutuwa da dama yayin taron wadan-nan sun hada da bayyanar da tushen matsalolin rashin tsaro da aikata laifuka a ji-har, kamar garkuwa da mutane, satar shanu, hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, da rikicin kabilanci, rawar da jami’an tsaro daban-daban na jihohi da cibiyoyin gargajiya suke takawa wajen yakar matsalolin, tallafin Majalisar Dinkin Duniya ga karfafa shari’a a aikata laifuka.

“Hanyoyi da yanayin da ke haifar wa al’umma shaye-shayen miyagun kwayoyi a Jihar Zamfara da wanda za a bi wajen rigakafin shan muggan kwayoyi da sauran muhimman batutuwa, duk an shirya su don tattaunawa a wannan taro.

“Ina kira ga mahalarta taron da su yi amfani da wannan damar kuma su ba da himma don cin gajiyar ayyukan. Ya kamata ku saurara, ku koya, kuma ku ba da gudunmawa mai inganci.

“A karshe, ina fatan dukkanin mahalarta taron za su kasance masu amfanar al’umma. Kamar yadda na bayyana, shawarwarin da aka samar a nan za su kasance masu muhimmanci wajen tsara dabarunmu da ayyukanmu don magance matsalolin da muke fuskanta.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BanditsInsurgencyKidnappersTsaroUnited NationsZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina So Na Ga Ina Kyautata Wa Iyayena Har Ma Da Bare

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 7 A Wani Sabon Hari A Jihar Neja

Related

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

3 days ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

3 days ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

1 week ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

1 week ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

1 week ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

2 weeks ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 7 A Wani Sabon Hari A Jihar Neja

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 7 A Wani Sabon Hari A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.