• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dokokin Kogi Ta Tsige Mataimakin Kakakin Majalisar, Ta Dakatar Da wasu 3

by Ahmed Muhammed Danasabe
3 years ago
Majalisar

Majalisar Dokokin Jihar Kogi ta tsige mataimakin shugaban majalisar kuma mamba mai wakiltar mazabar Ankpa ta Daya, Hon. Ahmed Muhammed daga mukaminsa.

A zaman gaggawa da ta gudanar a ranar Juma’a a birnin Lokoja, mambobin majalisar sun zargi Hon Ahmed Muhammed da sauran shugabannin majalisar guda uku da rashin nuna da’a da kuma yin amfani da ofisoshinsu ba bisa ka’ida ba.

  • 2023: Muna tattaunawa da Peter Obi kan yiwuwar hada takararmu — Kwankwaso 
  • ‘El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba’

Wani kudurin gaggawa da ya gabatar a zauren majalisar, dan majalisa mai wakiltar mazabar Dekina/Okura, Hon Enema Paul, ya ce ‘yan majalisar 17 cikin 25 da ke majalisar ne suka sanya hannun amincewa da tsige Hon Ahmed Muhammed da kuma dakatar da sauran shugabannin uku.

Shugabannin uku da aka dakatar daga majalisar da aka raba su da mukamansu, sun hada da Hon Bello Hassan Balogun (Shugaban masu rinjaye) da Hon Idris Ndako (Mataimakin masu rinjaye) da kuma Hon Edoko Moses Ododo (Mai tsawatarwa).

Kazalika, majalisar ta sanar da sunan Hon Alfa Momoh Rabi’u mai wakiltar mazabar Ankpa ta Biyu, a matsayin sabon mataimakin shugaban majalisar.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Sauran shugabannin majalisar da aka zaba sun hada da Hon Muktar Bajeh, a matsayin sabon shugaban masu rinjaye da Hon Umar Isah Tanimu wanda shi ne mataimakin shugaban masu rinjaye da Hon Ahmed Dahiru, a matsayin mai tsawatarwa na majalisar da kuma Hon Enema Paul, wanda zai kasance sabon mataimakin mai tsawatarwa na majalisar dokokin ta Jihar Kogi.

Tun da farko sai da shugaban majalisar, Hon Mathew Kolawole ya sanar da rushe dukkan kwamitocin majalisar.

An dai samar da kwararren matakan tsaro a harabar majalisar a yayin zaman.

‘Yan majalisa 17 cikin 25 ne suka halarci zaman majalisar na ranar Juma’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Zulum Ya Amince Da Daukar Likitoci 40 Aiki Don Tura su Karkara

Zulum Ya Amince Da Daukar Likitoci 40 Aiki Don Tura su Karkara

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.