ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dokokin Kogi Ta Tsige Mataimakin Kakakin Majalisar, Ta Dakatar Da wasu 3

by Ahmed Muhammed Danasabe
4 years ago
Majalisar

Majalisar Dokokin Jihar Kogi ta tsige mataimakin shugaban majalisar kuma mamba mai wakiltar mazabar Ankpa ta Daya, Hon. Ahmed Muhammed daga mukaminsa.

A zaman gaggawa da ta gudanar a ranar Juma’a a birnin Lokoja, mambobin majalisar sun zargi Hon Ahmed Muhammed da sauran shugabannin majalisar guda uku da rashin nuna da’a da kuma yin amfani da ofisoshinsu ba bisa ka’ida ba.

  • 2023: Muna tattaunawa da Peter Obi kan yiwuwar hada takararmu — Kwankwaso 
  • ‘El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba’

Wani kudurin gaggawa da ya gabatar a zauren majalisar, dan majalisa mai wakiltar mazabar Dekina/Okura, Hon Enema Paul, ya ce ‘yan majalisar 17 cikin 25 da ke majalisar ne suka sanya hannun amincewa da tsige Hon Ahmed Muhammed da kuma dakatar da sauran shugabannin uku.

ADVERTISEMENT

Shugabannin uku da aka dakatar daga majalisar da aka raba su da mukamansu, sun hada da Hon Bello Hassan Balogun (Shugaban masu rinjaye) da Hon Idris Ndako (Mataimakin masu rinjaye) da kuma Hon Edoko Moses Ododo (Mai tsawatarwa).

Kazalika, majalisar ta sanar da sunan Hon Alfa Momoh Rabi’u mai wakiltar mazabar Ankpa ta Biyu, a matsayin sabon mataimakin shugaban majalisar.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Sauran shugabannin majalisar da aka zaba sun hada da Hon Muktar Bajeh, a matsayin sabon shugaban masu rinjaye da Hon Umar Isah Tanimu wanda shi ne mataimakin shugaban masu rinjaye da Hon Ahmed Dahiru, a matsayin mai tsawatarwa na majalisar da kuma Hon Enema Paul, wanda zai kasance sabon mataimakin mai tsawatarwa na majalisar dokokin ta Jihar Kogi.

Tun da farko sai da shugaban majalisar, Hon Mathew Kolawole ya sanar da rushe dukkan kwamitocin majalisar.

An dai samar da kwararren matakan tsaro a harabar majalisar a yayin zaman.

‘Yan majalisa 17 cikin 25 ne suka halarci zaman majalisar na ranar Juma’a.

Majalisar
Ahmed Muhammed Danasabe
+ postsBio
  • Ahmed Muhammed Danasabe
    https://hausa.leadership.ng/author/ahmed-muhammed-danasabe/
    Da Ɗumi-ɗuminsa: Mai Martaba Ohinoyi na Kasar Ebira Ya Rasu
  • Ahmed Muhammed Danasabe
    https://hausa.leadership.ng/author/ahmed-muhammed-danasabe/
    Wa’adin Sauya Kudi: Yadda ‘Yan Nijeriya Suka Shiga Dimuwa
  • Ahmed Muhammed Danasabe
    https://hausa.leadership.ng/author/ahmed-muhammed-danasabe/
    Da Dumi-dumi: Bam Ya Tashi Gabanin Ziyarar Buhari A Jihar Kogi
  • Ahmed Muhammed Danasabe
    https://hausa.leadership.ng/author/ahmed-muhammed-danasabe/
    Sarkin Gumel Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Sarkin Lakwaja

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Zulum Ya Amince Da Daukar Likitoci 40 Aiki Don Tura su Karkara

Zulum Ya Amince Da Daukar Likitoci 40 Aiki Don Tura su Karkara

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.