ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

by Leadership Hausa
4 years ago
ASUU

Edita, don Allah ka ba ni fili a wannan jarida tamu mai farin jini don in kara sautin amon murya ta kan sauran muryoyin da ke ta kiraye-kiraye ga gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU game da yajin aikin da kungiyar ke yi tsawon kimanin watanni takwas kenan.

Yau kusan wata 8 kenan jami’oi a Nijeriya suke a kulle sakamakon rikicin da yaki ci yaki cinyewa tsakanin Gwamnati da ASUU, rikicin da ya sam oasali tun kusan 1999, an yi gwamnatoci da dama wadanda suke gadar wannan rikici kuma haka suke shudewa ba tare da kawo karshen shi ba, a namu bangarenmu dalibai wannan rikicin ba karamin cutar da rayuwarmu yake ba, domin duk lokacin da aka tafi irin wannan yajin aiki, komai na karatunmu tsayawa yake, kuma sannan da yawan mu komawa gida mukeyi muna zaman banza zaman jiran tsammani, saboda ko da mutum ya nemi wani abin yi dole sai dai ya zama na wucin gadi.

Tun daga lokacin da aka fara rikita rikita tsakanin gwamnatin tarayya da ASUU ba a taba yin gwamnati da dalibai muka sanya rai da tsammanin za ta kawo karshen wannan rikici ba, irin wannan gwamnati ta mai girma shugaban kasa Muhammad Buhari, hakan kuwa ya samo asali ne sakamakon irin kyautata mata zato da muke yi da kuma yadda muka ga tana yawan ambatawa a wajen yakin neman zabe cewa zata kula da rayuwar matasa, kuma zata bai wa harkar ilimi mahimmanci, amma sai dai kash gashi gwamnati tana shirin karewa lamarina kokarin chanjawa, a ranar 26 ga watan June, 2022 mun hango minister ma’aikata a fadar gwamanati da keAbuja, bayan kammala zaman Majalisar Ministoci watau FEC yana mana Albishir da cewa kusan komai ya zo karshe yanzu jira kawai suke yi hukumomin da abin ya shafa su tattara reports zuwa ranar laraba sai a yi sign, jin wannan labarin ya faranta mana rai sosai, ammah sai gashi mun ji shiru har zuwa yanzu.

ADVERTISEMENT

Wani abu da ya kara daga mana hankali sai ji muka yi a ranar Litinin 4 ga watan Yuli Shugaban Kungiyar ASUU yana wata magana mai kama da habaici, inda ya cewa “a shirye suke su jira gwamnati ta neme su ko da nan da shekara 2 ne, inda ya kara da cewa su da membobinsu zasu tuka mortar hanya, su siyar da gyada domin su samu abin da zasu ci ”Wannann maganar ta daga mana hankali gaskiya, domin duk dalibi na kwarai dole ya tausayawa malamansa tsawon wata 8 basu da Albashi, da wannan muke rokon gwamnatin tarayyah karkashin shugabancin Muhammadu Buhari, don Allah su tausayawa mana, su cika mana Alkawarin da Suka mana lokacin Campaign, Su tausayawa halin da yan uwanmu matasa ka iya fadawa sakamakon wannan dogon yajin Aiki.

Umar Kabir Dakata, marubuci ne kuma matashi mai sharhi kan harkokin ilimi da rayuwar matasa, shi ne kuma shugaban kungiyar Arewa Media Writers na Jihar Kano.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

ASUU
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba

Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.