• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

by Sulaiman and Abubakar Abba
1 year ago
IFAD

Wasu daga cikin manoman kasar nan, sun bukaci Shugaban Kasa; Bola Ahmed Tinubu, ya kara yawan adadin wadanda za su amfana a tallafin bunkasa aikin noma da gwamnatin tarayya ta kirkiro da shi a kasar. 

 

Sun gabatar da wannna bukatar ce, a makon da ya gabata a martanin da suka yi bayan jawabin da Shugaba Tinubu ya yi wa masu gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwar da barke a wasu daga cikin sasaan wannan kasa, inda shugaban ya shelantan cewa; zai samar wa da manoman kasar kayan habaka aikin noma.

  • Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Siyo Shinkafar Biliyan 14 Don Sayarwa A Farashi Mai Sauki

A cewar manoman, alkawarin da shugaba Tinubu ya yi na habaka fannin noma a kasar, ko kadan bai isa ba; har sai idan ya sanya miliyoyin manoman kasar a cikin shirye-shiryen gwamnatinsa na bunkasa fannin.

 

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Daya daga cikin manyan manoma a kasar kuma shugaban kungiyar dilolin sayar da kayan manoma na kasa (NAIDA), Kabir Umar Fara ya bayyana cewa, kamata ya yi gwamnatin ta yi abin da ya dara haka.

 

Kabir ya ci gaba da cewa, tallafin da gwamnatin za ta bayar; ba zai wani taka kara ba, domin ba zai isa ga manoma sama da 200’000 da ke daukacin jihohi 36 na kasar nan ba; ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

 

Haka zalika, shugaban ya yi kira ga Shugaba Tinubu; da ya jawo masu ruwa da tsaki da sauran kungiyoyin manoma, musamman domin su fahimci kalubalen da manoman kasar ke ci gaba da fuskanta, domin a samar musu da goyon bayan da ya kamata.

 

A cewarsa, a lokacin noman rani; kimanin manoman Alkama 200,000 ne aka taimaka wa da kuma karin wasu manoman ranin kimanin 100’000.

 

Ya kara da cewa, akwai kuma bukatar a taimaka wa kimanin kananan manoma 200,000, inda ya yi nuni da cewa; idan har ana so a samar da dauki a fannin aikin noman, manoman kasar za su iya samar da kashi 25 a cikin dari na amfanin gona a kasar, inda kuma gwamnatin za ta samar da rangwamen da ya kai kashi 75 cikin dari; wanda hakan zai kai har zuwa ga sauran manyan manoma.

 

Har ila yau, ya yi nuni da cewa; a halin yanzu buhun takin zamani daya na samfarin NPK kudinsa ya kai kimanin Naira 45,000, ya ake so kuma manomi ya iya sayen sa a kan wannan farashin?

 

Kabiru ya kara da cewa, da za a ci gaba da tsarin noma irin na tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari, manoman kasar nan za su iya sayen kayan aikin noma a cikin farashi mai sauki.

 

Shi ma a nasa bangaren, shugaban kungiyar manoma na kasa (AFAN), Kabiru Ibrahim ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya ba ta da wadatattun kudaden da za su kai ga sauran kananan manoma, amma kamata ya yi ta samar da kyakkyawan yanayi ga manoman kasar, domin samun damar kara habaka fannin.

 

Shi kuwa shugaban kungiyar masu sarrafawa da sayar da takin gargajiya na kasa (OFPSAN) Noel Keyen, ya nuna damuwarsa a kan ayyana dokar ta-baci da gwamnatin shugaba Tinubu ta yi, a fannin aikin noman kasar; amma ta gaza zuba wadatattun kudaden da suka kamata a cikin shirin na habaka fannin.

 

Kazalika, Keyen ya kuma nuna damuwarsa a kan yadda gwamnatin ta gaza samawar wa da musamman kananan manoma kayan aikin noma.

 

Shi ma shugaban masu sarrafawa da sayar da takin zamani na kasa (FEPSAN), Sadik Kassim yaba wa shirin samar da tallafin kayan aikin noma da ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci suka wanzar na shirye-shiryen aikin noma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Next Post
Ma’aikatar Tsaron Gidan Kasar Sin: Amurka Na Yunkurin Nuna Fin Karfinta Bisa Amfani Da Makamashin Nukiliya

Ma’aikatar Tsaron Gidan Kasar Sin: Amurka Na Yunkurin Nuna Fin Karfinta Bisa Amfani Da Makamashin Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.