ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

by Sulaiman and Abubakar Abba
2 years ago
IFAD

Wasu daga cikin manoman kasar nan, sun bukaci Shugaban Kasa; Bola Ahmed Tinubu, ya kara yawan adadin wadanda za su amfana a tallafin bunkasa aikin noma da gwamnatin tarayya ta kirkiro da shi a kasar. 

 

Sun gabatar da wannna bukatar ce, a makon da ya gabata a martanin da suka yi bayan jawabin da Shugaba Tinubu ya yi wa masu gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwar da barke a wasu daga cikin sasaan wannan kasa, inda shugaban ya shelantan cewa; zai samar wa da manoman kasar kayan habaka aikin noma.

ADVERTISEMENT
  • Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Siyo Shinkafar Biliyan 14 Don Sayarwa A Farashi Mai Sauki

A cewar manoman, alkawarin da shugaba Tinubu ya yi na habaka fannin noma a kasar, ko kadan bai isa ba; har sai idan ya sanya miliyoyin manoman kasar a cikin shirye-shiryen gwamnatinsa na bunkasa fannin.

 

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Daya daga cikin manyan manoma a kasar kuma shugaban kungiyar dilolin sayar da kayan manoma na kasa (NAIDA), Kabir Umar Fara ya bayyana cewa, kamata ya yi gwamnatin ta yi abin da ya dara haka.

 

Kabir ya ci gaba da cewa, tallafin da gwamnatin za ta bayar; ba zai wani taka kara ba, domin ba zai isa ga manoma sama da 200’000 da ke daukacin jihohi 36 na kasar nan ba; ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

 

Haka zalika, shugaban ya yi kira ga Shugaba Tinubu; da ya jawo masu ruwa da tsaki da sauran kungiyoyin manoma, musamman domin su fahimci kalubalen da manoman kasar ke ci gaba da fuskanta, domin a samar musu da goyon bayan da ya kamata.

 

A cewarsa, a lokacin noman rani; kimanin manoman Alkama 200,000 ne aka taimaka wa da kuma karin wasu manoman ranin kimanin 100’000.

 

Ya kara da cewa, akwai kuma bukatar a taimaka wa kimanin kananan manoma 200,000, inda ya yi nuni da cewa; idan har ana so a samar da dauki a fannin aikin noman, manoman kasar za su iya samar da kashi 25 a cikin dari na amfanin gona a kasar, inda kuma gwamnatin za ta samar da rangwamen da ya kai kashi 75 cikin dari; wanda hakan zai kai har zuwa ga sauran manyan manoma.

 

Har ila yau, ya yi nuni da cewa; a halin yanzu buhun takin zamani daya na samfarin NPK kudinsa ya kai kimanin Naira 45,000, ya ake so kuma manomi ya iya sayen sa a kan wannan farashin?

 

Kabiru ya kara da cewa, da za a ci gaba da tsarin noma irin na tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari, manoman kasar nan za su iya sayen kayan aikin noma a cikin farashi mai sauki.

 

Shi ma a nasa bangaren, shugaban kungiyar manoma na kasa (AFAN), Kabiru Ibrahim ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya ba ta da wadatattun kudaden da za su kai ga sauran kananan manoma, amma kamata ya yi ta samar da kyakkyawan yanayi ga manoman kasar, domin samun damar kara habaka fannin.

 

Shi kuwa shugaban kungiyar masu sarrafawa da sayar da takin gargajiya na kasa (OFPSAN) Noel Keyen, ya nuna damuwarsa a kan ayyana dokar ta-baci da gwamnatin shugaba Tinubu ta yi, a fannin aikin noman kasar; amma ta gaza zuba wadatattun kudaden da suka kamata a cikin shirin na habaka fannin.

 

Kazalika, Keyen ya kuma nuna damuwarsa a kan yadda gwamnatin ta gaza samawar wa da musamman kananan manoma kayan aikin noma.

 

Shi ma shugaban masu sarrafawa da sayar da takin zamani na kasa (FEPSAN), Sadik Kassim yaba wa shirin samar da tallafin kayan aikin noma da ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci suka wanzar na shirye-shiryen aikin noma.

Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Sulaiman
    Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
Manoma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Ma’aikatar Tsaron Gidan Kasar Sin: Amurka Na Yunkurin Nuna Fin Karfinta Bisa Amfani Da Makamashin Nukiliya

Ma’aikatar Tsaron Gidan Kasar Sin: Amurka Na Yunkurin Nuna Fin Karfinta Bisa Amfani Da Makamashin Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.