ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

by Sulaiman and Abubakar Abba
2 years ago
IFAD

Wasu daga cikin manoman kasar nan, sun bukaci Shugaban Kasa; Bola Ahmed Tinubu, ya kara yawan adadin wadanda za su amfana a tallafin bunkasa aikin noma da gwamnatin tarayya ta kirkiro da shi a kasar. 

 

Sun gabatar da wannna bukatar ce, a makon da ya gabata a martanin da suka yi bayan jawabin da Shugaba Tinubu ya yi wa masu gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwar da barke a wasu daga cikin sasaan wannan kasa, inda shugaban ya shelantan cewa; zai samar wa da manoman kasar kayan habaka aikin noma.

ADVERTISEMENT
  • Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Siyo Shinkafar Biliyan 14 Don Sayarwa A Farashi Mai Sauki

A cewar manoman, alkawarin da shugaba Tinubu ya yi na habaka fannin noma a kasar, ko kadan bai isa ba; har sai idan ya sanya miliyoyin manoman kasar a cikin shirye-shiryen gwamnatinsa na bunkasa fannin.

 

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Daya daga cikin manyan manoma a kasar kuma shugaban kungiyar dilolin sayar da kayan manoma na kasa (NAIDA), Kabir Umar Fara ya bayyana cewa, kamata ya yi gwamnatin ta yi abin da ya dara haka.

 

Kabir ya ci gaba da cewa, tallafin da gwamnatin za ta bayar; ba zai wani taka kara ba, domin ba zai isa ga manoma sama da 200’000 da ke daukacin jihohi 36 na kasar nan ba; ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

 

Haka zalika, shugaban ya yi kira ga Shugaba Tinubu; da ya jawo masu ruwa da tsaki da sauran kungiyoyin manoma, musamman domin su fahimci kalubalen da manoman kasar ke ci gaba da fuskanta, domin a samar musu da goyon bayan da ya kamata.

 

A cewarsa, a lokacin noman rani; kimanin manoman Alkama 200,000 ne aka taimaka wa da kuma karin wasu manoman ranin kimanin 100’000.

 

Ya kara da cewa, akwai kuma bukatar a taimaka wa kimanin kananan manoma 200,000, inda ya yi nuni da cewa; idan har ana so a samar da dauki a fannin aikin noman, manoman kasar za su iya samar da kashi 25 a cikin dari na amfanin gona a kasar, inda kuma gwamnatin za ta samar da rangwamen da ya kai kashi 75 cikin dari; wanda hakan zai kai har zuwa ga sauran manyan manoma.

 

Har ila yau, ya yi nuni da cewa; a halin yanzu buhun takin zamani daya na samfarin NPK kudinsa ya kai kimanin Naira 45,000, ya ake so kuma manomi ya iya sayen sa a kan wannan farashin?

 

Kabiru ya kara da cewa, da za a ci gaba da tsarin noma irin na tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari, manoman kasar nan za su iya sayen kayan aikin noma a cikin farashi mai sauki.

 

Shi ma a nasa bangaren, shugaban kungiyar manoma na kasa (AFAN), Kabiru Ibrahim ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya ba ta da wadatattun kudaden da za su kai ga sauran kananan manoma, amma kamata ya yi ta samar da kyakkyawan yanayi ga manoman kasar, domin samun damar kara habaka fannin.

 

Shi kuwa shugaban kungiyar masu sarrafawa da sayar da takin gargajiya na kasa (OFPSAN) Noel Keyen, ya nuna damuwarsa a kan ayyana dokar ta-baci da gwamnatin shugaba Tinubu ta yi, a fannin aikin noman kasar; amma ta gaza zuba wadatattun kudaden da suka kamata a cikin shirin na habaka fannin.

 

Kazalika, Keyen ya kuma nuna damuwarsa a kan yadda gwamnatin ta gaza samawar wa da musamman kananan manoma kayan aikin noma.

 

Shi ma shugaban masu sarrafawa da sayar da takin zamani na kasa (FEPSAN), Sadik Kassim yaba wa shirin samar da tallafin kayan aikin noma da ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci suka wanzar na shirye-shiryen aikin noma.

Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
Manoma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Ma’aikatar Tsaron Gidan Kasar Sin: Amurka Na Yunkurin Nuna Fin Karfinta Bisa Amfani Da Makamashin Nukiliya

Ma’aikatar Tsaron Gidan Kasar Sin: Amurka Na Yunkurin Nuna Fin Karfinta Bisa Amfani Da Makamashin Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.