ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

by Sulaiman and Abubakar Abba
2 years ago
IFAD

Wasu daga cikin manoman kasar nan, sun bukaci Shugaban Kasa; Bola Ahmed Tinubu, ya kara yawan adadin wadanda za su amfana a tallafin bunkasa aikin noma da gwamnatin tarayya ta kirkiro da shi a kasar. 

 

Sun gabatar da wannna bukatar ce, a makon da ya gabata a martanin da suka yi bayan jawabin da Shugaba Tinubu ya yi wa masu gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwar da barke a wasu daga cikin sasaan wannan kasa, inda shugaban ya shelantan cewa; zai samar wa da manoman kasar kayan habaka aikin noma.

ADVERTISEMENT
  • Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Siyo Shinkafar Biliyan 14 Don Sayarwa A Farashi Mai Sauki

A cewar manoman, alkawarin da shugaba Tinubu ya yi na habaka fannin noma a kasar, ko kadan bai isa ba; har sai idan ya sanya miliyoyin manoman kasar a cikin shirye-shiryen gwamnatinsa na bunkasa fannin.

 

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Daya daga cikin manyan manoma a kasar kuma shugaban kungiyar dilolin sayar da kayan manoma na kasa (NAIDA), Kabir Umar Fara ya bayyana cewa, kamata ya yi gwamnatin ta yi abin da ya dara haka.

 

Kabir ya ci gaba da cewa, tallafin da gwamnatin za ta bayar; ba zai wani taka kara ba, domin ba zai isa ga manoma sama da 200’000 da ke daukacin jihohi 36 na kasar nan ba; ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

 

Haka zalika, shugaban ya yi kira ga Shugaba Tinubu; da ya jawo masu ruwa da tsaki da sauran kungiyoyin manoma, musamman domin su fahimci kalubalen da manoman kasar ke ci gaba da fuskanta, domin a samar musu da goyon bayan da ya kamata.

 

A cewarsa, a lokacin noman rani; kimanin manoman Alkama 200,000 ne aka taimaka wa da kuma karin wasu manoman ranin kimanin 100’000.

 

Ya kara da cewa, akwai kuma bukatar a taimaka wa kimanin kananan manoma 200,000, inda ya yi nuni da cewa; idan har ana so a samar da dauki a fannin aikin noman, manoman kasar za su iya samar da kashi 25 a cikin dari na amfanin gona a kasar, inda kuma gwamnatin za ta samar da rangwamen da ya kai kashi 75 cikin dari; wanda hakan zai kai har zuwa ga sauran manyan manoma.

 

Har ila yau, ya yi nuni da cewa; a halin yanzu buhun takin zamani daya na samfarin NPK kudinsa ya kai kimanin Naira 45,000, ya ake so kuma manomi ya iya sayen sa a kan wannan farashin?

 

Kabiru ya kara da cewa, da za a ci gaba da tsarin noma irin na tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari, manoman kasar nan za su iya sayen kayan aikin noma a cikin farashi mai sauki.

 

Shi ma a nasa bangaren, shugaban kungiyar manoma na kasa (AFAN), Kabiru Ibrahim ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya ba ta da wadatattun kudaden da za su kai ga sauran kananan manoma, amma kamata ya yi ta samar da kyakkyawan yanayi ga manoman kasar, domin samun damar kara habaka fannin.

 

Shi kuwa shugaban kungiyar masu sarrafawa da sayar da takin gargajiya na kasa (OFPSAN) Noel Keyen, ya nuna damuwarsa a kan ayyana dokar ta-baci da gwamnatin shugaba Tinubu ta yi, a fannin aikin noman kasar; amma ta gaza zuba wadatattun kudaden da suka kamata a cikin shirin na habaka fannin.

 

Kazalika, Keyen ya kuma nuna damuwarsa a kan yadda gwamnatin ta gaza samawar wa da musamman kananan manoma kayan aikin noma.

 

Shi ma shugaban masu sarrafawa da sayar da takin zamani na kasa (FEPSAN), Sadik Kassim yaba wa shirin samar da tallafin kayan aikin noma da ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci suka wanzar na shirye-shiryen aikin noma.

Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Manoma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Ma’aikatar Tsaron Gidan Kasar Sin: Amurka Na Yunkurin Nuna Fin Karfinta Bisa Amfani Da Makamashin Nukiliya

Ma’aikatar Tsaron Gidan Kasar Sin: Amurka Na Yunkurin Nuna Fin Karfinta Bisa Amfani Da Makamashin Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.