• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Alkama 50,000 Suka Samu Tallafi A Jihohi 13 —FMAN

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Alkama 50,000 Suka Samu Tallafi A Jihohi 13 —FMAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu sarrafa fulawa ta Nijeriya (FMAN) ta ce ta samar da cibiyoyin saye da sayarwa a jihohi 13, domin kawar da dukkan hatsin da ke tattare da noman wanda ya kunshi manoma 50,000 a shekara ta 2022-2023.

Manajan na shirin bunkasa alkama na FMAN Dakta Aliyu Sama’ila ne ya bayyana haka a lokacin bikin ranar noman alkama a karamar hukumar Bunza daje jihar ta Kebbi.

  • Zama Lafiya Ya Fi Zama Dan Sarki
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Matsayinta Na Warware Matsalar Ukraine A Siyasance

Ya ce aikinsu na daya shi ne samar da kasuwa ga manoman alkama a kasar nan. “Mun noma kadada 200 na alkama a shekarar 2022, kuma yanzu mun ninka shi zuwa 400 a bana a jihar Kebbi.

Haka kuma “Muna fadada sayayyarmu a matsayin masana’antu a duk fadin jihohin da ke noman alkama ta hanyar karin ma’aikatan tarawa da karfin ajiya.

“Musamman, mun kafa cibiyoyin siyar da kayayyaki a fadin jihohin Arewa 13 don cire duk wani hatsin alkama daga manoma 50,000 a jahohin.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

“Jihohin su ne Kano da Kaduna da Jigawa da Kebbi da Sakkwato da Bauchi da Adamawa da Gombe da Filato da Taraba da Zamfara da kuma Yobe.

Kazalika “Don ci gaba da fadada noman alkama a kasar nan, dole ne mu kara yawan amfanin gonakin manoma, don sanya alkama ta yi gogayya da shinkafa da sauran noman rani,” in ji  Dakta Sama’ila.

Ya ce noman gonakin masu girman hekta 114 a fadin jihohin Arewa shida, domin ba da horo kan aikin noma na daga cikin shirinsu na ci gaba. Jihohin sun hada da Adamawa da Borno da Gombe da Filato da Taraba da Yobe.

“Za mu fadada shirin FMAN na kai tsaye tare da ba da lamuni don bai wa manoma 4,300 a fadin hekta 3,900 a jihohi bakwai, wato, Kano da Jigawa da Sakkwato da Kebbi da Kaduna da Binuwai da Zamfara.

“Za kuma mu fadada samar da iri tare da wasu kamfanoni shida da suka tabbatar da iri, wadanda suka hada da noman rani da damina, don samar da isasshen iri na hekta 10,000 a kakar da sauransu,” in ji shi.

Har ilayau Dakta Aliyu Samaila ya kara da cewa IMPAN ta shiga tsakani wajen siyan alkama fiye da ton 50,000 a cikin shekaru 5 da suka gabata tare da sanya hannu kan yarjejeniyar sayan kowace irin alkama da ake samu a farashi mai kyau bisa ga amfanin noma da manoman.

Bugu da kari “Mun sayi alkama kai tsaye daga sama da manoma 4,000 a cibiyoyin noman alkama 40 a cikin 2022.  Ya ci gaban da cewa “Mun bayar da tallafin iri da taki da sinadarai masu amfani ga manoma 400 a shekarar 2019 da kuma manoma 700 a shekarar 2020 a jihohin Kano, Jigawa da Kebbi.

Da yake jawabi a madadin manoman, Shugaban WFAN na yankin Karamar hukumar Bunza, Alhaji Umar Abdullahi, ya yabawa FMAN kan shirin bunkasa alkama da nufin bunkasa noma a kasar nan.

Ya ce shiga tsakani da kungiyar ta yi ya baiwa manoma da dama kwarin gwiwar shiga noman alkama a jihar kebbi.

Ya kara da cewa manoman suna fuskantar sabbin dabarun noma da kuma kyawawan dabi’un noma domin bunkasa nomansu.

“Muna fatan yin hadin gwiwa tare da FMAN a duk fadin darajar don inganta yawan amfanin da muke samu ta hanyar iri masu inganci, fadada ayyukanmu, da kuma inganta hanyoyin samar da ban ruwa,” in ji Umar Abdullahi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiManomaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Miyar Ijjah

Next Post

PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

2 days ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.