• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Alkama 50,000 Suka Samu Tallafi A Jihohi 13 —FMAN

by Abubakar Abba
3 years ago
Manoma

Kungiyar masu sarrafa fulawa ta Nijeriya (FMAN) ta ce ta samar da cibiyoyin saye da sayarwa a jihohi 13, domin kawar da dukkan hatsin da ke tattare da noman wanda ya kunshi manoma 50,000 a shekara ta 2022-2023.

Manajan na shirin bunkasa alkama na FMAN Dakta Aliyu Sama’ila ne ya bayyana haka a lokacin bikin ranar noman alkama a karamar hukumar Bunza daje jihar ta Kebbi.

  • Zama Lafiya Ya Fi Zama Dan Sarki
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Matsayinta Na Warware Matsalar Ukraine A Siyasance

Ya ce aikinsu na daya shi ne samar da kasuwa ga manoman alkama a kasar nan. “Mun noma kadada 200 na alkama a shekarar 2022, kuma yanzu mun ninka shi zuwa 400 a bana a jihar Kebbi.

Haka kuma “Muna fadada sayayyarmu a matsayin masana’antu a duk fadin jihohin da ke noman alkama ta hanyar karin ma’aikatan tarawa da karfin ajiya.

“Musamman, mun kafa cibiyoyin siyar da kayayyaki a fadin jihohin Arewa 13 don cire duk wani hatsin alkama daga manoma 50,000 a jahohin.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

“Jihohin su ne Kano da Kaduna da Jigawa da Kebbi da Sakkwato da Bauchi da Adamawa da Gombe da Filato da Taraba da Zamfara da kuma Yobe.

Kazalika “Don ci gaba da fadada noman alkama a kasar nan, dole ne mu kara yawan amfanin gonakin manoma, don sanya alkama ta yi gogayya da shinkafa da sauran noman rani,” in ji  Dakta Sama’ila.

Ya ce noman gonakin masu girman hekta 114 a fadin jihohin Arewa shida, domin ba da horo kan aikin noma na daga cikin shirinsu na ci gaba. Jihohin sun hada da Adamawa da Borno da Gombe da Filato da Taraba da Yobe.

“Za mu fadada shirin FMAN na kai tsaye tare da ba da lamuni don bai wa manoma 4,300 a fadin hekta 3,900 a jihohi bakwai, wato, Kano da Jigawa da Sakkwato da Kebbi da Kaduna da Binuwai da Zamfara.

“Za kuma mu fadada samar da iri tare da wasu kamfanoni shida da suka tabbatar da iri, wadanda suka hada da noman rani da damina, don samar da isasshen iri na hekta 10,000 a kakar da sauransu,” in ji shi.

Har ilayau Dakta Aliyu Samaila ya kara da cewa IMPAN ta shiga tsakani wajen siyan alkama fiye da ton 50,000 a cikin shekaru 5 da suka gabata tare da sanya hannu kan yarjejeniyar sayan kowace irin alkama da ake samu a farashi mai kyau bisa ga amfanin noma da manoman.

Bugu da kari “Mun sayi alkama kai tsaye daga sama da manoma 4,000 a cibiyoyin noman alkama 40 a cikin 2022.  Ya ci gaban da cewa “Mun bayar da tallafin iri da taki da sinadarai masu amfani ga manoma 400 a shekarar 2019 da kuma manoma 700 a shekarar 2020 a jihohin Kano, Jigawa da Kebbi.

Da yake jawabi a madadin manoman, Shugaban WFAN na yankin Karamar hukumar Bunza, Alhaji Umar Abdullahi, ya yabawa FMAN kan shirin bunkasa alkama da nufin bunkasa noma a kasar nan.

Ya ce shiga tsakani da kungiyar ta yi ya baiwa manoma da dama kwarin gwiwar shiga noman alkama a jihar kebbi.

Ya kara da cewa manoman suna fuskantar sabbin dabarun noma da kuma kyawawan dabi’un noma domin bunkasa nomansu.

“Muna fatan yin hadin gwiwa tare da FMAN a duk fadin darajar don inganta yawan amfanin da muke samu ta hanyar iri masu inganci, fadada ayyukanmu, da kuma inganta hanyoyin samar da ban ruwa,” in ji Umar Abdullahi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Manoma

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.