• Leadership Hausa
Monday, May 29, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Alkama 50,000 Suka Samu Tallafi A Jihohi 13 —FMAN

by Abubakar Abba
3 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Alkama 50,000 Suka Samu Tallafi A Jihohi 13 —FMAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu sarrafa fulawa ta Nijeriya (FMAN) ta ce ta samar da cibiyoyin saye da sayarwa a jihohi 13, domin kawar da dukkan hatsin da ke tattare da noman wanda ya kunshi manoma 50,000 a shekara ta 2022-2023.

Manajan na shirin bunkasa alkama na FMAN Dakta Aliyu Sama’ila ne ya bayyana haka a lokacin bikin ranar noman alkama a karamar hukumar Bunza daje jihar ta Kebbi.

  • Zama Lafiya Ya Fi Zama Dan Sarki
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Matsayinta Na Warware Matsalar Ukraine A Siyasance

Ya ce aikinsu na daya shi ne samar da kasuwa ga manoman alkama a kasar nan. “Mun noma kadada 200 na alkama a shekarar 2022, kuma yanzu mun ninka shi zuwa 400 a bana a jihar Kebbi.

Haka kuma “Muna fadada sayayyarmu a matsayin masana’antu a duk fadin jihohin da ke noman alkama ta hanyar karin ma’aikatan tarawa da karfin ajiya.

“Musamman, mun kafa cibiyoyin siyar da kayayyaki a fadin jihohin Arewa 13 don cire duk wani hatsin alkama daga manoma 50,000 a jahohin.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

Nijeriya Ce Ta Daya A Noman Gero Ta Uku A Noman Gyada A Duniya – Farfesa Gaya

“Jihohin su ne Kano da Kaduna da Jigawa da Kebbi da Sakkwato da Bauchi da Adamawa da Gombe da Filato da Taraba da Zamfara da kuma Yobe.

Kazalika “Don ci gaba da fadada noman alkama a kasar nan, dole ne mu kara yawan amfanin gonakin manoma, don sanya alkama ta yi gogayya da shinkafa da sauran noman rani,” in ji  Dakta Sama’ila.

Ya ce noman gonakin masu girman hekta 114 a fadin jihohin Arewa shida, domin ba da horo kan aikin noma na daga cikin shirinsu na ci gaba. Jihohin sun hada da Adamawa da Borno da Gombe da Filato da Taraba da Yobe.

“Za mu fadada shirin FMAN na kai tsaye tare da ba da lamuni don bai wa manoma 4,300 a fadin hekta 3,900 a jihohi bakwai, wato, Kano da Jigawa da Sakkwato da Kebbi da Kaduna da Binuwai da Zamfara.

“Za kuma mu fadada samar da iri tare da wasu kamfanoni shida da suka tabbatar da iri, wadanda suka hada da noman rani da damina, don samar da isasshen iri na hekta 10,000 a kakar da sauransu,” in ji shi.

Har ilayau Dakta Aliyu Samaila ya kara da cewa IMPAN ta shiga tsakani wajen siyan alkama fiye da ton 50,000 a cikin shekaru 5 da suka gabata tare da sanya hannu kan yarjejeniyar sayan kowace irin alkama da ake samu a farashi mai kyau bisa ga amfanin noma da manoman.

Bugu da kari “Mun sayi alkama kai tsaye daga sama da manoma 4,000 a cibiyoyin noman alkama 40 a cikin 2022.  Ya ci gaban da cewa “Mun bayar da tallafin iri da taki da sinadarai masu amfani ga manoma 400 a shekarar 2019 da kuma manoma 700 a shekarar 2020 a jihohin Kano, Jigawa da Kebbi.

Da yake jawabi a madadin manoman, Shugaban WFAN na yankin Karamar hukumar Bunza, Alhaji Umar Abdullahi, ya yabawa FMAN kan shirin bunkasa alkama da nufin bunkasa noma a kasar nan.

Ya ce shiga tsakani da kungiyar ta yi ya baiwa manoma da dama kwarin gwiwar shiga noman alkama a jihar kebbi.

Ya kara da cewa manoman suna fuskantar sabbin dabarun noma da kuma kyawawan dabi’un noma domin bunkasa nomansu.

“Muna fatan yin hadin gwiwa tare da FMAN a duk fadin darajar don inganta yawan amfanin da muke samu ta hanyar iri masu inganci, fadada ayyukanmu, da kuma inganta hanyoyin samar da ban ruwa,” in ji Umar Abdullahi.

Tags: KebbiManomaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Miyar Ijjah

Next Post

PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

Related

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista
Noma Da Kiwo

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

6 hours ago
Nijeriya Ce Ta Daya A Noman Gero Ta Uku A Noman Gyada A Duniya – Farfesa Gaya
Noma Da Kiwo

Nijeriya Ce Ta Daya A Noman Gero Ta Uku A Noman Gyada A Duniya – Farfesa Gaya

2 days ago
Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Edo Suke Kokawa
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Edo Suke Kokawa

1 week ago
Gwamntin Tarayya Da Ta Ogun Sun Fara Yi Wa Dabbobi Allurar Riga-kafin Cuttutuka
Noma Da Kiwo

Gwamntin Tarayya Da Ta Ogun Sun Fara Yi Wa Dabbobi Allurar Riga-kafin Cuttutuka

1 week ago
Yunkurin Masu Ruwa Da Tsaki A Nahiyar Afirka Wajen Samar Da Takin Zamani
Noma Da Kiwo

Yunkurin Masu Ruwa Da Tsaki A Nahiyar Afirka Wajen Samar Da Takin Zamani

2 weeks ago
Hukumar Abinci Ta Duniya Ta Ce A Karon Farko Farashin Abinci Ya Tashi
Noma Da Kiwo

Hukumar Abinci Ta Duniya Ta Ce A Karon Farko Farashin Abinci Ya Tashi

2 weeks ago
Next Post
PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

An Rantsar Da Gwamna Bala Muhammad A Matsayin Gwamnan Bauchi A Karo Na 2

An Rantsar Da Gwamna Bala Muhammad A Matsayin Gwamnan Bauchi A Karo Na 2

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Jagoranci Za Mu Yi Ba Mulkin ‘Yan Nijeriya Ba – Tinubu

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

May 29, 2023
A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

May 29, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

May 29, 2023
Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

May 29, 2023
Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

May 29, 2023
Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

May 29, 2023
Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

May 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.