ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Tumatur 70,000 Na Bukatar Tallafin Gwamnatin Kano – Yadakwari

by Mustapha Ibrahim
2 years ago
Kano

Shugaban kungiyar manoman tumatur reshen Jihar Kano, Alhaji Dan Ladi Sani Yadakwari ya bayyana cewa, yanzu haka manoman tumatur sama da dubu 70 da ke Jihar Kano na bukatar tallafi daga sabon gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusif (Abba Gida- gida) na tsaga dam-dam wato madatsun ruwa da ake da su a jihar wanda marigayi Alhaji Audu Bako ya yi su sama da shekara 50 da suka gabata.

A cewarsa, yin haka zai sa a samu guraran noman rani wadatattu a Jihar Kano da zai sa dubban matasan su samu aikin yi a wannan lokaci.

  • Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno
  • Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Nadin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Yadakwari ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishin kungiyar manoman tumatur da ke Jihar Kano ranar Litinin da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa akwai bukatar gwamnan Kano ya nemi hadin kan Shugaban Kasa, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu da sauran masu ruwa da tsaki na tabbatar an hana shigo da tumatur daga kasashen ketarer.

Ya ce be shigowa da tumatir a Nijeriya ne dalilin da ya sa manoma ba sa nomansa yadda ta kamata har ya yi karanci, wanda hakan ce ta sa ya yi tsada da sauran kayan miya.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

Haka kuma ya ce tsare-tsaren na tallafa wa manoma a gwamnatin baya tun daga matakin jiha da na tarayya abun a yaba ne kan kokarinsu na bunkasa noma a Kano da ma Nijeriya, musamman ma tsarin bunkasa noma na bai wa manoma rance ‘Anchor barrow’, wanda ya sa manoma da dama da suka san yadda ake abun suka samu duk da wasu masu shaci fadi a rediyo na cewa ba a bai wa wadanda suka dace ba.

“Shawararmu dai ga gwamnatocin kasar nan shi ne, a fito da tsarin ba da bashi ko tallafi a lokacin kaka wato lokacin girbi ta yadda za a bai wa mutum bashi gwargwadon abun da ya noma aka gani idan ma kara mai za a yi kashi 50 ko 100. Idan kuma ragi za a yi masa a kan abun da za a ba shi sai a yi hakan cikin tsari.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

DSS
Labarai

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS
Labarai

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe
Labarai

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Next Post
Xi Ya Nanata Bukatar Samun Ci Gaba Mai Inganci A Fannin Tsaron Intanet Da Aikin Sadarwa

Xi Ya Nanata Bukatar Samun Ci Gaba Mai Inganci A Fannin Tsaron Intanet Da Aikin Sadarwa

LABARAI MASU NASABA

DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.