• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manta Tarihi Ya Sa Nijeriya Cikin Halin kaka-ni-ka-yi

by Murtala Muhammad
3 years ago
in Rahotonni
0
Manta Tarihi Ya Sa Nijeriya Cikin Halin kaka-ni-ka-yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Ku tashi mu farka ‘yan Arewa Ku san bacci aikin kawai ne” in ji Marigayi Dakta Alhaji Mamman Shata Katsina.

Wannan shi ne baitin wakar da marigayi Alhaji Dakta Mamman Shatan Waka, Shata Katsina mawakin Arewa ya yi domin tunasar da mu abin da ya kamata mu yi a matsayin mu na ‘yan Nijeriya ya kamata mu sani, to yanzu an wayi gari Arewa na cikin yanayin dimuwa da tashin hankali a kan yadda Nijeriyarmu ke tafiya a matakin rashin tsaro da rashin sanin makomar kasar a kakar zaben 2023 da ke fuskantowa, talaka da masu hannu da shuni da mahukuntan kasar ba mu da wata kasa da muke alfahari da ita tamkar wannan kasar.

  • Sabon Fim din JAMILA Zai Fara Haskawa A Makon Nan –Hafsat Sa’eed
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

Shin me ya sa talaka zai zuba ido a kan wani abin da bai taka kara ya karya ba ko kuma a ce wasu ‘yan canjin Nairori da za a bashi a yayin zabe ya kuma bayar da kasar tamu ta gado ga hannun ‘yan jari hujja wadanda su ba kasar ce a gabansu ba.

Idan ba a manta ba, a lokacin da jam’iyyar APC ke babban gangaminta na farko a Abuja a kafin zaben shekarar 2015, Audu Ogbe ya hau Mimbari ya shelanta wa talaka cewa ‘BringBackOurGirl,’ kungiyarsu ce, kuma suna goyon bayan abubuwan da take.

Yau kuma an wayi gari ita dai jam’iyyar ta APC ta ki amincewa da duk wata kungiya ko wasu gungun al’umma da za su fito domin su nuna ranshin goyon ko rashin jin dadin tsarin mulkin da take gudanarwa a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

A shekarar 2006 da 2007, lokacin da Tsohon Gwamnan Jihar Kano Malam Ibrahim Shekarau ke kokarin yakin neman zabensa karo na biyu na wa’adin mulkinsa, an samu wani gagarumin tashin hankalin da ya faru a wannan tsakanin na kisan babban Shehin Malami Sheikh Malam Ja’afar Mahmud Adam, wanda wannan ne sanadiyyar bullar wata kungiya mai suna Taliban a wancan lokacin a Jihar Kano dake da’awar cewa ana kashe manyan Malamai a kasar kuma hukuma ba ta daukar mataki a kan hakan ba.

Wannan ya sa suka zo domin fada da jami’an tsaro, al’ummar gari suka goyi da bayansu, aka kuma basu hadin kai wanda wannan ya sa suka ci karensu ba babbaka a kan jami’an tsaro, inda suka kai farmaki a wuraren kamar irinsu ofisoshin ‘yan sandan Sharada da na Fanshekara, inda suka yada zango, kuma suka yi sansani a nan unguwar ta Fanshekara, hakan ya jawo har mazauna unguwar ta Fanshekara yin gudun hijira zuwa cikin gari, bayan wani lokacin da bai wuce kwana uku zuwa hudu ba, kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano ya fito ya shelanta cewa su dai sun yi nasarar korarsu daga jihar, amma babu takamaiman yadda aka yi suka bar jihar, dama ba mutanen Kano ba ne, zuwa suka yi jihadi a cewarsu.

Daga bayan nan mutanen Nijeriya suke zargin cewa kamar wannan kungiya da ta yi da’awar jihadi a wancan lokacin ita ce ta shirya kuma ta gudanar da kisan Malam Ja’afar. Haka kuma ita wannan kungiya ita ce ta rikidide zuwa kungiyar Boko Haram da take ayyukan ta’addancinta a tsakanin Arewa maso Gabashin Nijeriya, gefen Chadi, gefen Kamaru da kuma gefen kasar Nijar.

Tarihi kuma bai manta da ita wannan kungiya na da’awar cewa karatun Boko Haramun ne, amma kuma da suka fara fada da hukumomin tsaron gwamnati daga baya kuma sai suka koma kan mai uwa da wabi, kan duk wani dan Nijeriyar da baya goya musu baya, kuma har yanzu sun kasa ba da hujjar da ta sa suke takama da ita na cewa ilimin Boko haramun ne.

Yan’ Nijeriya, mu kula, mu gane cewa duk wata takama da muke yi, muna yin ta ne sakamakon zaman lafiya da kuma gagarumar gudunmawar da jami’an tsaron kasar Nijeriya ke bamu, amma idan kuma muka zuba ido ‘yan ta’adda suka ci gaba da keta wa jami’an tsaron Nijeriya haddi to wallahi wannan kwanciyar hankalin da zaman lafiyar da muke takama da su sai ta zame mana kunci da bakin ciki, don da an gama da su kan ‘yan Nijeria da basu san hawa da sauka ba za a dawo, mu talakawan Nijeriyar da bamu da wata kasar da tafi Nijeriya.

Menene dalilin da ya sa talaka ke goyon bayan cin mutumcin jami’an tsaron Nijeriya, shin shi jami’in tsaro wani mutum ne daban ba iri daya da mutane ba, ko shi ba daga cikin mu ya fito ba, idan kuma daga cikin mu ya fito me ya sa muke goya wa ‘yan ta’adda baya su ci mutunci jami’ansu, kada talaka ya manta shi fa jami’in tsaro, da ne kamar dan kowa, kuma uba ne kamar yadda uban kowa yake, kuma yayan wasu ne kuma kanin wasu ne.

Abin da talaka kullum yake manta wa shi ne, shi fa jami’in tsaro mutum ne wanda ya sadaukar da jin dadinsa da jininsa don talaka ya kwanta cikin aminci ya tashi cikin aminci da kwanciyar hankali, jami’in tsaro ne da ya sadaukar da jininsa da lokacinsa domin tsaron dukiyoyi da rayukan ‘yan kasa, mu talakawa mu yi hobbasa domin taimaka wa jami’an tsaron kasar nan, tun daga matakin dansanda, soja da dukkan wani dogari mai damara da mara damara duk suna bukatar gudunmuwarmu talakawan Nijeriya domin su gudanar da aikin su kamar yadda ya kamata.

Ita kuma gwamnati ita ce da babbar gudunmuwar bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar Nijeriya. Hakki ne da ya rataya a wuyan gwamnatin Nijeriya ta tabbata ta sauke dukkan nauyin jami’an tsaron da ya rataya a wuyan ta, babu yadda za a yi ka dauki mutum aiki kuma ka bashi makami kuma ka barshi da yunwa, har yanzu ina neman sanin shin kasafin kudin da ake gabatarwa majalisar kasa kowacce shekara shin ko sun taba bin diddigin kasafin kudin jami’an tsaron Nijeriya sun ga tabbacin abubuwan da aka saka cikin an tanadar musu kudin ko kuma kayan aikin da aka ce za a tanadar musu a cikin kasafin ya tabbata?.

Me ya sa ba a tanadar wa jami’an tsaro kayan aikin na zamani ba, gwamnati ki taimaka ki kula da kasafin kudin jami’an tsaro da lafiyarsu, da matsuguni, da magunguna a asibitocinsu, domin zaman lafiya da kwanciyar hankalinsu shi ne kula da tsaron kasarmu.

Ku tuna fa ‘yan Nijeriya Jami’an tsaro su ne, suka zaunar da Nijeriya a matsayin gamayya Nijeriya, ba don jajircewarsu ba da tuni wani labarin ake ba wannan ba, ko lokacin da Ojukwu ya yi tawaye jami’an tsaro ne suka hana shi tabbatar da kudurinsa na fasa Nijeriya gida biyu domin kafa kasar Biafara, talaka ya kalli tarihi ko don taimaka wa jami’an tsaro. Tarihi na da muhimmanci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramHalin Kaka-ni-ka-yikanoMatsalar TsaroShugabanniTa'addanciYanayi
ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Cafke Dillalan Makamai A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Next Post

Gwamnati Ta Shure Yarjejeniyarmu, Yanzu Ba Mu San Alkiblarmu Ba – IKMAN

Related

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

1 day ago
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

2 days ago
Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano
Rahotonni

Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

2 days ago
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

1 week ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

1 week ago
Next Post
Gwamnati Ta Shure Yarjejeniyarmu, Yanzu Ba Mu San Alkiblarmu Ba – IKMAN

Gwamnati Ta Shure Yarjejeniyarmu, Yanzu Ba Mu San Alkiblarmu Ba – IKMAN

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.