ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

by Sadiq
4 years ago
CDD

Cibiyar Dimokuradiyya da Ci Gaba ta (CDD), ta yi Allah-wadai da cin tarar Naira miliyan biyar da Hukumar Yada Labarai ta Kasa (NBC) ta yi ga gidan talabijin na Trust TV da wasu kafafen yada labarai uku, saboda watsa shirye-shiryen da suka shafi ‘yan ta’adda.

Trust TV mallakin kamfanin Media Trust Group ne,kamfanin da ke buga jaridun Daily Trust, Aminiya da sauransu.

  • Mu Kula Da Wayoyin Da Ke Hannun Yara
  • Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

Haka nan NBC ta ci tarar kamfanin Multichoice Nigeria Limited, mamallakan DSTV, TelCom Satellite Limited (TSTV) da NTA-Startimes Limited, saboda watsa wani shiri da hukumar yada labarai ta BBC ta yi mai taken, ‘Bandits Warlords Of Zamfara’.

ADVERTISEMENT

CDD, a cikin wata sanarwa a ranar Asabar da Daraktarta, Idayat Hassan ta fitar, ta bayyana sanya tarar a matsayin abin zalunci, inda ta bukaci hukumar ta janye matakinta cikin gaggawa.

A cewar Hassan, tarar wani yunkuri ne na cin mutuncin kafafen yada labarai da kuma tauye hakkin ‘yan kasa na fadin albarkacin bakinsu da yada labarai.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mun yin Allah wadai da kakkausar murya kan tarar da Hukumar Yada Labarai ta Kasa (NBC) ta yi ga gidan talabijin na Trust TV da sauran kafafen yada labarai.

“Mun yi mamakin daukar matakin ba tare da bai wa kafafen yada labaran da abin ya shafa lokaci ba don mayar da martani don kare kansu.

“A matsayinmu na abokan aikin gidan talabijin na Trust TV wajen shirya shirin, ba tare da neman afuwa ba mun jaddada cewa an yi shirin ne kuma an watsa shi ne domin amfanin jama’a. An gina shirin ne bisa tsawon shekaru da aka shafe ana gudanar da bincike a fagen, wanda ke wakiltar dukkanin al’ummomin da abin ya shafa da kuma samar da hanyoyin kawo karshen rikicin.

“Yayin da babban zaben 2023 ke karatowa, muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta guji yin duk wani abu da zai kawo barazana ga harkar yada labarai ko kuma tauye ‘yancin fadin albarkacin baki da ‘yancin ‘yan kasa.”

MASU ALAKA

Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti
Manyan Labarai

Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti

June 22, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

June 22, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
Labarai

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026
Next Post
An Nemi Jam’iyyar APC Ta kara kaimi Wajen Biyan Bukatun ‘Yan Nijeriya

An Nemi Jam'iyyar APC Ta kara kaimi Wajen Biyan Bukatun 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti

Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

June 22, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.