• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Abubuwan Da Ke Gaban Majalisa Ta 10 Bayan Dawowa Hutu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Manyan Abubuwan Da Ke Gaban Majalisa Ta 10 Bayan Dawowa Hutu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan majalisar tarayya da suka yi hutun makwanni biyu, sun ci gaba da zama a ranar Talata 4 ga watan Yuli don fara aikin majalisa gadan-gadan.

Majalisar dattawa da ta wakilai dai sun dage zama bayan ‘yan kwanaki da rantsar da sabbin shugabanninsu har zuwa ranar 4 ga watan Yuli domin samun damar ba da mukamai da ofisoshi ga masu dawowa da kuma sabbin ‘yan majalisa.

  • Bukatar Dakatar Da Kara Kudin Wutar Lantarki A Nijeriya
  • Kamfanin Meta Mamallakin Facebook Ya Yi Wa Twitter Kishiya

Kafin tafiya hutun, majalisun biyu sun zauna a takaice bayan an gudanar da zabukan da aka fafata. A zaben da aka yi na shugabannin majalisar ta 10, ’yan takarar jam’iyyar APC ne suka samu nasara duk da barazanar da wasu ‘ya`yan jam’iyyar da na ‘yan adawa suka yi cewa ba za su amince da dauki-dora ba.

A bangare zauren majalisar wakilai kuwa, Hon. Tajudeen Abass daga Jihar Kaduna da Hon. Benjamin Kalu daga Jihar Abiya ne suka yi nasara a matsayin shugaban majalisar wakilai da mataimaki.

Yayin da suke shirin bude sabon babi na zaman majalisan bayan dawowa daga hutu, ana sa rai za su yi aiki tukuru wajen tunkarar muhimman batutuwan da suka shafi kasa da wasu ayyukan da ba a kammala ba. Abu na farko da majalisun biyu suka yi shi ne sanar da wadanda za su taya su gudanar da aikin majalisar a mukamai daban-daban.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana sunayen wadanda aka nada a manyan mukamai na majalisar dattawa ta 10.

Daga cikin wadanda aka nada sun hada da Sanata Opeyemi Bamidele a matsayin shugaban masu rinjaye na majalisar. Bamidele na wakiltar Ekiti ta tsakiya a majalisar dattawa. Sauran sun hada da Sanata Dabid Umahi mai wakiltar Ebonyi ta Kudu a matsayin mataimakin shugaban masu rinjaye.

Ya yin da Sanata Mohammed Ali Ndume, mai wakiltar Borno ta Kudu, ya zama mai tsawatarwa a majalisar dattawa, Sanata Lola Ashiru, mai wakiltar Kwara ta Kudu a matsayin mataimakin mai tsawatarwa.

Akpabio ya ce an nada su a mukaman ne bisa yarjejeniya.

Hakazalika, a zauren majalisar wakilai, shugaban majalisar Tajudeen Abbas ya sanar da Julius Ihonbbere daga Jihar Edo a matsayin shugaban masu rinjaye na majalisar da kuma Usman Kumo daga Jihar Gombe a matsayin mai tsawatarwa na majalisar.

Abbas ya kuma bayyana Halims Abdulahi daga Kogi a matsayin mataimakin shugaban masu rinjaye da Oriyomi Onanuga daga Ogun a matsayin mataimakin mai tsawatarwa.

Kingsley Chinda daga Jihar Ribas shi ne aka ba shugaban marasa rinjaye, sai Ali Isah daga Jihar Gombe a matsayin mai tsawatarwa na marasa rinjaye da Madaki Aliyu daga Jihar Kano a matsayin mataimakin shugaban marasa rinjaye da George Adegeye daga Jihar Legas da ya zama mataimakin shugaban marasa rinjaye.

Sai dai kuma, kamar tsugune ba ta kare ba, saboda jam’iyyar APC mai mulki ta nesanta kanta da wannan zabi na wadanda aka bai wa mukamai a majalisar, a hannu guda kuma gwamnonin jam’iyyar suka ce suna goyon bayan shugabannin majalisar kan zabinsu. Ba a dai san yadda za ta kaya ba sai nan gaba.

A halin da ake ciki kuma, akwai babban jan aiki da ke gaban majalisun musamman ta fuskar nada kwamitoci da shugabanninsu:

  • Rikicin Shugabancin Kwamitoci

Ana sa ran shugabannin majalisun guda biyu za su bayyana shugabanni da mambobin kwamitoci. Akwai rahotannin ce-ce-ku-ce a tsakanin ‘yan majalisar kan neman shugabanci da mambobin kwamitoci.

Haka kuma manyan ‘yan majalisa suna fafutukar neman samun kwamitoci masu gwabi da mukamai da suka fi daraja.

A daidai lokacin da aka zabi shugaban majalisar dattawa, Akpabio daga yankin kudu maso kudu, mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau daga yankin Arewa maso yamma, shugaban majalisar wakilai, Abbas daga yankin Arewa maso yamma da mataimakin shugaban majalisar wakilai, Kalu daga yankin Kudu maso gabas, ’yan majalisa daga wasu shiyyoyi musamman Arewa maso gabas da Arewa ta tsakiya na kokawa kan ba su kananan mukamai a zauren majalisun. A halin yanzu an mayar da hankali a ga su wane ne za a nada a kwamitoci masu tsoka wadanda za su yi aiki a bangaren mai da kudade da sauran harkokin tattalin arziki, sannan su wane ne za a bari da fafutuka a kwamitocin sassan da ba su da maiko.

  • Batun Rashin Tsaro Da Tabbatar Da Nadin Shugabannin Hafsoshin Tsaro

A majalissar da ta gabata, batutuwan da suka shafi tsaro a ko da yaushe su ne ginshikin abubuwan da ake tattauwa a zauren majalisar dattawa da na wakilai, saboda wasu kudurori da suka shafi tsaro da ‘yan majalisar suka yi.

Sai dai kuma a yanzu tsaron kasar na kara tabarbarewa a kowace rana saboda sabbin hare-haren da ‘yan ta’adda ke kaiwa a arewa maso gabas da arewa maso yamma har ma da kudu maso yamma. Ana sa ran majalisar dokokin kasar ta 10 za ta fito da wasu dabaru da za su taimaka wa bangaren zartarwa na gwamnati wajen dakile matsalar rashin tsaro.

Ana sa ran ‘yan majalisar tarayya za su ci gaba da tantance sabbin shugabannin hafsoshin tsaro da sufeto janar na ‘yansanda da kuma shugaban hukumar kwastam da Shugaba Bola Tinubu ya nada kwanan nan.

Wadanda aka nada za su ci gaba da yin aiki ne a kan mukamansu, har sai majalisar dokokin kasar ta tabbatar da su. Za su bayyana a gaban kwamitin tsaro lokacin da aka kafa.

Sanatocin da za su ci gaba da zama kuma za su tantance wadanda aka nada a matsayin ministoci da zarar an mika sunayensu ga majalisar dattawa domin tabbatar da su.

  • Ajandar Majalisun

Ana sa ran dukkan majalisun biyu za su bayyana ajandodinsu, inda za su bayyana abubuwan da za su fi ba da muhimmanci wanda za su mayar da hankali a cikin shekaru hudu masu zuwa.

Shugaban majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, a jawabinsa na ranar kaddamar da majalisar ya ce a karkashinsa, majalisa ta 10 za ta dora har ta zarce nasarorin da aka samu a zauren majalisa ta 9.

Ya ce majalisar ta 10 za ta gabatar da gyare-gyare da sabbin abubuwa don amfanin ‘yan Nijeriya. Ya kara da cewa nan da ‘yan makonni kadan, sabuwar majalisar wakilai za ta fitar da ajandarta da ta tsara.

Ana sa ran shugabannin ba za su yi kasa a gwiwa ba.  Ana tsammani zauren majalisun na 10 su kasance ba a taba samun irinsu ba a tarihin majalisar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KalubaleMajalisa Ta 10Rashin Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gobe Tinubu Zai Tafi Guinea-Bissau Halartar Taron ECOWAS

Next Post

Ma’aikatar Kudin Sin: Ainihin Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Ita Ce Cimma Moriyar Juna

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

13 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Majalisa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Ma’aikatar Kudin Sin: Ainihin Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Ita Ce Cimma Moriyar Juna

Ma’aikatar Kudin Sin: Ainihin Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Ita Ce Cimma Moriyar Juna

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Majalisa

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.