• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Manyan Labarai
0
Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin Majalisar Dattijai na gyaran kundin tsarin mulkin 1999 ya fara wani taron tattaunawar kwanaki biyu a Kano, tare da nufin kammala aikin gyaran kundin tsarin mulki kafin watan Disamba 2025.

Taron, wanda aka shirya tare da haɗin gwuiwar Cibiyar Tsarin Dokoki da Inganta Siyasa (PLAC), na da nufin magance batutuwan da suka haɗa da ƴancin ƙananan hukumomi, da kafa ƴansandan jihohi, da kuma bai wa Sarakunan gargajiya dama a gwamnatance domin magance matsalar tsaro.

  • Sanata Barau Jibrin Ya Ƙaddamar Da Motocin Zirga-Zirga A Kano
  • Jihar Kano Ta Musanta Zargin Karɓar Bashin Biliyan 177 Daga Faransa

Masu jawabi, ciki har da Sanata Jibrin Barau, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai, sun jaddada mahimmancin haɗin kai da masu ruwa da tsaki kamar gwamnoni, da majalisun jihohi, da ɓangaren shari’a, da ƙungiyoyin farar hula domin tabbatar da samun nasarar wannan gyara.

Barau ya yi kira da a samar da hadin kai tsakanin dukkan ɓangarorin majalisar dokoki guda biyu sannan ya buƙaci a yi la’akari sosai da shawarwarin da za su kawo canji mai ɗorewa ga al’ummar Nijeriya.

Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, ya jaddada mahimmancin ɗaukar mataki cikin lokaci da kuma tsara ayyuka yadda ya dace domin kaucewa karkatar da hankalin jama’a yayin da zaɓe ke gabatowa.

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Kwamitocin majalisar dattijai da na wakilai sun shirya gudanar da tarukan sauraron ra’ayoyin jama’a tare da Sarakunan gargajiya da shugabannin siyasa domin samun cikakken bayani.

Sauran masu jawabi, ciki har da Hon. Adebo Edward Ogundoyin, Shugaban Taron Shugabannin Majalisun Jihohi, da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, sun buƙaci a mayar da hankali kan ƴancin mata, da ƴancin ƙananan hukumomi, da kuma rawar da Sarakuna zasu iya takawa a hukumance.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Barau JibrinConstitutionkanoTraditional Rulers
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Manchester City Za Ta Kai Bantenta Babu Rodri?

Next Post

Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

1 hour ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

7 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

9 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

11 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

13 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

1 day ago
Next Post
Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya

Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.