• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa

by Sulaiman
3 days ago
in Labarai
0
Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, a ranar Alhamis ya bada sanarwar wani gagarumin shiri na Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, wanda ya bada damar karɓar albashi har ƙarshen rayuwa ga duk wani babban jami’i da ya yi ritaya daga ma’aikatar a matsayin Mataimakin Kwanturola, Kwanturola, ko Kwamanda-Janar zuwa sama.

 

Ministan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a Babban Taron Bita na Ministan na shekarar 2025 a Abuja, inda ya bayyana nasarorin Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida tare da nanata sadaukarwar ta ga aiwatar da sauye-sauye da ƙarfafa wa ma’aikata gwiwa a hukumomin da ke ƙarƙashin ta.

  • AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea
  • Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

Hukumomin da za su amfana da wannan tsari a ma’aikatar su ne: Hukumar Gyaran Hali (wato ta gidajen yari), Hukumar Shige-da-Fice (NIS), Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya(FFS), da Hukumar Tsaro ta farin kaya (NSCDC).

 

Labarai Masu Nasaba

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

Wannan bayani yana ƙunshe ne a cikin sanarwar da Jami’in Yaɗa Labarai na Ƙasa (PRO) na Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, DCF P.O. Abraham, ya fitar jim kaɗan bayan taron bitar.

 

Ya ce: “Ministan ya bayyana matuƙar godiya ga Shugaba Tinubu bisa ga ɗimbin goyon bayan sa, yana mai tabbatar da cewa dukkan hukumomin da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida suna amfana da albarkatun da ke cikin Shirin Sabunta Fata.”

 

Tunji-Ojo ya ci gaba da lissafa manyan nasarorin ma’aikatar, waɗanda suka haɗa da kammala aikin ƙarin girman ma’aikata wanda aka daɗe ba a yi ba, ya ce sama da ma’aikata 50,000 ne aka yi wa ƙarin girma a cikin shekaru biyu da suka gabata.

 

Haka kuma ya ce daga yanzu ba za a riƙa yin ƙarin girma bisa matakin daɗewa a aiki ba, sai dai bisa iya aiki da kuma dagewa, ya nanata cewa ma’aikatar ta ƙudiri aniyar yi wa kowane ma’aikaci sakayya bisa ga ƙoƙarin da ya yi a aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Baki Kusan 50 Daga Kasashe 30 Na Turai Za Su Halarci Bikin Tunawa Da Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa Kan Zaluncin Japanawa

Next Post

Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?

Related

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas
Labarai

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

5 hours ago
Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan
Labarai

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

6 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Labarai

Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-ƙasa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna – Gwamnati

10 hours ago
Kwale-kwale
Labarai

Haɗarin Kwale-kwale Ya Ci Rayukan Mutane 15 A Zamfara

11 hours ago
Sin Za Ta Kare Moriyarta Ta Hanyar Mayar Da Martani Game Da Sabon Matakin Kakaba Harajin Kwastan Da Amurka Ke Dauka
Labarai

Trump Ya Kakaba Kashi 50 Kan Indiya Saboda Sayen Kaya Daga Rasha

11 hours ago
An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 
Manyan Labarai

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 

12 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?

Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

August 31, 2025
Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

August 31, 2025
Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

August 31, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

August 31, 2025
Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

August 31, 2025
Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

August 31, 2025
Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

August 31, 2025
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

August 31, 2025
Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

August 31, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-ƙasa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna – Gwamnati

August 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.