ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Nanjing

Alal hakika, tarihi ba zai taba mantawa da kisan kiyashi da sojojin mamaya na kasar Japan suka yi a birnin Nanjing na kasar Sin ba. Muggan laifukan yaki da dakarun na Japan suka aikata cikin kwanaki sama da 40 bayan mamaye birnin a ranar 13 ga watan Disamban shekarar 1937 sun yi matukar muni.

Tarihi ya tabbatar da cewa, dakarun na Japan sun hallaka fararen hula Sinawa da dakaru marasa dauke da makamai da yawansu ya haura 300,000, tare da yi wa sama da mata 20,000 fyade. An kuma fayyace wadannan muggan ayyuka cikin kundayen tarihi yadda ya kamata.

To sai dai kuma sabanin abun da ake zato, cewa bangaren Japan zai ci gaba da neman afuwa, da nuna nadamar wadannan abubuwa da suka faru a baya, sai ga shi wasu kafofin watsa labaran kasar na furta wasu kalamai na kokari musanta tarihi.

ADVERTISEMENT

A wata makala da aka wallafa ranar Litinin din farkon makon nan, editan wata jaridar kasar Japan ya soki wani fim mai suna Dead to Rights, wanda ya yi bitar irin cin zarafin da sojojin Japan suka aikatawa Sinawa fararen hula a wancan lokaci. Har ma dan jaridar ya ce wai batun kisan kiyashi na Nanjing labarin yaudara ne kawai da kasar Sin ta kitsa. Lallai irin wadannan kalamai masu ban mamaki suna da munin gaske, suna kuma dada karfafa zargin da aka dade ana yiwa bangaren Japan na karyata hakikanin tarihi, da nufin sauya gaskiya, da kaucewa daukar alhakin abubuwan da suka faru.

Tun bayan fitar da Dead to Rights a Sin da sauran sassan duniya, fim din ya samu matukar karbuwa, kasancewar ya yi “Waiwaye Adon Tafiya” game da munin ta’asar da dakarun Japan suka aikata a birnin Nanjing a wancan lokaci. To, amma abun tambayar shi ne me ya sa har yanzu wasu masu ra’ayin rikau na Japan ke kokarin kore abubuwan da fim din ya nuna? Amsar wannan tambaya a bayyane take, irin wadannan Japanawa suna tsoron kara bayyanar gaskiya!

LABARAI MASU NASABA

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Yanzu haka a nan kasar Sin ana ta shirye-shiryen gudanar da babban bikin cika shekaru 80 da cimma nasarar yaki da mamayar sojojin Japan, da nasarar yakin kin tafarkin murdiya, wanda shi ma wani lokaci ne da zai dada tabbatarwa duniya zahirin abubuwan da suka wakana, tare da karyata sassan dake kokarin lullube gaskiya, da kaucewa daukar alhakin ta’asar da aka aikawa al’ummar Sin a yayin mamayar birnin Nanjing.

Nanjing
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya
Nanjing
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
  • Sulaiman
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

MASU ALAKA

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Next Post
Ranar Hausa: Masana Sun Bayyana Bunkasa Da Tasirin Harshen A Duniya

Ranar Hausa: Masana Sun Bayyana Bunkasa Da Tasirin Harshen A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.