• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kasuwannin Da Aka Fi Samun Goruba A Nijeriya

by Abubakar Abba
3 years ago
in Sana'a Sa'a
0
Manyan Kasuwannin Da Aka Fi Samun Goruba A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Goruba, a turance ana kiranta da Doum palm fruits an kuma hakikance cewa, goruba, ta samu asali ne daga kasar Masar, amma a yanzu ana iya shuka ta a gurare da dama, ciki har da Nijeriya.

Goruba na yin bishiya ne, inda ake tsinkar ‘ya’yanta domin ci, ko kuma a sarrafa ta zuwa wani naucin abinci.

  • Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane
  • Da ÆŠumi-É—uminsa: Kwamishina Bunkasa Kasuwanci Da Masana’antu Na Jigawa Ya Rasu

Manyan Kasuwannin Da Aka Fi Samun Goruba A Nijeriya:

Ana samun goruba a kasuwar Gamboru da ke cikin garin Maiduguri a jihar Borno, inda a wannan kasuwar ake zuwa ana siyenta da yawa domin yin safararta zuwa wasu jihohin kasar nan.

Bugu da kari, akwai kuma wasu manyan kasuwannin a kasar nan da ake yin hadahadar kasuwancin goruba.

Labarai Masu Nasaba

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

Ana Hada-hadar Kasuwancin Goruba A Wasu kananan Kasuwanni:

A wasu kananan kasuwannin da ke fadin kasar nan, ana yin hada-hadar kasuwancin goruba, domin mutane da dama, ciki har da manyan mutane suna zuwa domin su siya.

Haka su ma yara suna siyen busasshiyar goruba domin ci, wasu kuma yaran na siyenta domin tafiya da ita makaranta don ci ganin cewa tana taimaka musu kamar abinci.

Ana samun goruba a kasuwannin unguwani da ke cikin gari ko kuma a wasu shaguna haka wasu su kan yi tallarta a kan hanya.

A yankin Arewa maso gabas, da ke cikin kasar nan, Allah ya albarkaci yankin da goruba mai yawa.

Goruba na da dandano mai dadi, musamman mutanen da ke zaune a yankunan da ke da zafi, suna yin amfani da goruba, ganin, tana taimaka wa yanayin jikin ‘yan’adam.

Ana Sarrafata Wajen Hada Abinci:

Ana sarrafa goruba wajen hada ta a cikin abinci, ta hanyar saka ta a cikin ruwa ko kuma a cikin ruwan zafi har zuwa wasu ‘yan mintuna, ganin cewa, tana dauke da sinadaran da ke gina jikin ‘yan’adam.

Har ila yau, ana sarrafa goruba wajen hada shayi, haka ana sarrafa goruba wajen yin kayan lemon Kwalba don a samu dandano.

Amfanin Goruba Ga Kiwon Lafiyar ‘Yan’adam:

Masana a fannin kiwon lafiya sun bayyana cewa, goruba na taimaka wa kiwon lafiyar ‘yan’adam, musamman ganin cewa, tana da sinadarin fiber, haka kuma tana taimaka wa wajen rage karfin ciwon suga.

Bugu da kari, busasshiyar goruba na taimaka wa musu fama da ciwon suga da saurin narkar da abincin da mutun ya ci, haka tana dauke da sinadarin carbohydrate da kuma bitamins B.

Har ila yau, masu ilimi a fannin kiwon lafiya sun yi ittafakin cewa, goruba na taimaka wa wajen kara bunkasa aikin kwakwalwar ’yan’adam.

Goruba dai, na girma a jikin bishiya inda wasu ki ciro danyarta don su busar da ita, wasu kuma ke barinta a jikin bishiyar sai ta bushe da kanta kafin su cire ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmfaniGorubaKasuwanciKiwon LafiyaNijeriyaSana"a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane

Next Post

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

Related

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera
Sana'a Sa'a

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera

4 months ago
Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi
Labarai

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

7 months ago
Akwai Dimbin Alhairi A Harkar Kasuwanci Na Kirifto – Khadija Ahmad
Labarai

Akwai Dimbin Alhairi A Harkar Kasuwanci Na Kirifto – Khadija Ahmad

9 months ago
Dangote Ya Soki Sabon Tsarin Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Dangote Ya Soki Sabon Tsarin Gwamnatin Tinubu

11 months ago
Shara
Sana'a Sa'a

Sarrafa Daskararriyar Shara

2 years ago
Halin Da Masu Kananan Sana’o’i Ke Ciki (3)
Sana'a Sa'a

Halin Da Masu Kananan Sana’o’i Ke Ciki (3)

2 years ago
Next Post
Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al'umma A Kagara – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.