ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kasuwannin Da Aka Fi Samun Goruba A Nijeriya

by Abubakar Abba
4 years ago
Goruba

Goruba, a turance ana kiranta da Doum palm fruits an kuma hakikance cewa, goruba, ta samu asali ne daga kasar Masar, amma a yanzu ana iya shuka ta a gurare da dama, ciki har da Nijeriya.

Goruba na yin bishiya ne, inda ake tsinkar ‘ya’yanta domin ci, ko kuma a sarrafa ta zuwa wani naucin abinci.

  • Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane
  • Da Ɗumi-ɗuminsa: Kwamishina Bunkasa Kasuwanci Da Masana’antu Na Jigawa Ya Rasu

Manyan Kasuwannin Da Aka Fi Samun Goruba A Nijeriya:

ADVERTISEMENT

Ana samun goruba a kasuwar Gamboru da ke cikin garin Maiduguri a jihar Borno, inda a wannan kasuwar ake zuwa ana siyenta da yawa domin yin safararta zuwa wasu jihohin kasar nan.

Bugu da kari, akwai kuma wasu manyan kasuwannin a kasar nan da ake yin hadahadar kasuwancin goruba.

LABARAI MASU NASABA

Aure Ba Ya Ruƙuwa Sai Da Sana’a

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Ana Hada-hadar Kasuwancin Goruba A Wasu kananan Kasuwanni:

A wasu kananan kasuwannin da ke fadin kasar nan, ana yin hada-hadar kasuwancin goruba, domin mutane da dama, ciki har da manyan mutane suna zuwa domin su siya.

Haka su ma yara suna siyen busasshiyar goruba domin ci, wasu kuma yaran na siyenta domin tafiya da ita makaranta don ci ganin cewa tana taimaka musu kamar abinci.

Ana samun goruba a kasuwannin unguwani da ke cikin gari ko kuma a wasu shaguna haka wasu su kan yi tallarta a kan hanya.

A yankin Arewa maso gabas, da ke cikin kasar nan, Allah ya albarkaci yankin da goruba mai yawa.

Goruba na da dandano mai dadi, musamman mutanen da ke zaune a yankunan da ke da zafi, suna yin amfani da goruba, ganin, tana taimaka wa yanayin jikin ‘yan’adam.

Ana Sarrafata Wajen Hada Abinci:

Ana sarrafa goruba wajen hada ta a cikin abinci, ta hanyar saka ta a cikin ruwa ko kuma a cikin ruwan zafi har zuwa wasu ‘yan mintuna, ganin cewa, tana dauke da sinadaran da ke gina jikin ‘yan’adam.

Har ila yau, ana sarrafa goruba wajen hada shayi, haka ana sarrafa goruba wajen yin kayan lemon Kwalba don a samu dandano.

Amfanin Goruba Ga Kiwon Lafiyar ‘Yan’adam:

Masana a fannin kiwon lafiya sun bayyana cewa, goruba na taimaka wa kiwon lafiyar ‘yan’adam, musamman ganin cewa, tana da sinadarin fiber, haka kuma tana taimaka wa wajen rage karfin ciwon suga.

Bugu da kari, busasshiyar goruba na taimaka wa musu fama da ciwon suga da saurin narkar da abincin da mutun ya ci, haka tana dauke da sinadarin carbohydrate da kuma bitamins B.

Har ila yau, masu ilimi a fannin kiwon lafiya sun yi ittafakin cewa, goruba na taimaka wa wajen kara bunkasa aikin kwakwalwar ’yan’adam.

Goruba dai, na girma a jikin bishiya inda wasu ki ciro danyarta don su busar da ita, wasu kuma ke barinta a jikin bishiyar sai ta bushe da kanta kafin su cire ta.

Goruba
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Aure Ba Ya Ruƙuwa Sai Da Sana’a
Labarai

Aure Ba Ya Ruƙuwa Sai Da Sana’a

January 24, 2026
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC
Sana'a Sa'a

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera
Sana'a Sa'a

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera

February 1, 2025
Next Post
Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al'umma A Kagara – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.