ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kasuwannin Da Aka Fi Samun Goruba A Nijeriya

by Abubakar Abba
4 years ago
Goruba

Goruba, a turance ana kiranta da Doum palm fruits an kuma hakikance cewa, goruba, ta samu asali ne daga kasar Masar, amma a yanzu ana iya shuka ta a gurare da dama, ciki har da Nijeriya.

Goruba na yin bishiya ne, inda ake tsinkar ‘ya’yanta domin ci, ko kuma a sarrafa ta zuwa wani naucin abinci.

  • Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane
  • Da Ɗumi-ɗuminsa: Kwamishina Bunkasa Kasuwanci Da Masana’antu Na Jigawa Ya Rasu

Manyan Kasuwannin Da Aka Fi Samun Goruba A Nijeriya:

ADVERTISEMENT

Ana samun goruba a kasuwar Gamboru da ke cikin garin Maiduguri a jihar Borno, inda a wannan kasuwar ake zuwa ana siyenta da yawa domin yin safararta zuwa wasu jihohin kasar nan.

Bugu da kari, akwai kuma wasu manyan kasuwannin a kasar nan da ake yin hadahadar kasuwancin goruba.

LABARAI MASU NASABA

Aure Ba Ya Ruƙuwa Sai Da Sana’a

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Ana Hada-hadar Kasuwancin Goruba A Wasu kananan Kasuwanni:

A wasu kananan kasuwannin da ke fadin kasar nan, ana yin hada-hadar kasuwancin goruba, domin mutane da dama, ciki har da manyan mutane suna zuwa domin su siya.

Haka su ma yara suna siyen busasshiyar goruba domin ci, wasu kuma yaran na siyenta domin tafiya da ita makaranta don ci ganin cewa tana taimaka musu kamar abinci.

Ana samun goruba a kasuwannin unguwani da ke cikin gari ko kuma a wasu shaguna haka wasu su kan yi tallarta a kan hanya.

A yankin Arewa maso gabas, da ke cikin kasar nan, Allah ya albarkaci yankin da goruba mai yawa.

Goruba na da dandano mai dadi, musamman mutanen da ke zaune a yankunan da ke da zafi, suna yin amfani da goruba, ganin, tana taimaka wa yanayin jikin ‘yan’adam.

Ana Sarrafata Wajen Hada Abinci:

Ana sarrafa goruba wajen hada ta a cikin abinci, ta hanyar saka ta a cikin ruwa ko kuma a cikin ruwan zafi har zuwa wasu ‘yan mintuna, ganin cewa, tana dauke da sinadaran da ke gina jikin ‘yan’adam.

Har ila yau, ana sarrafa goruba wajen hada shayi, haka ana sarrafa goruba wajen yin kayan lemon Kwalba don a samu dandano.

Amfanin Goruba Ga Kiwon Lafiyar ‘Yan’adam:

Masana a fannin kiwon lafiya sun bayyana cewa, goruba na taimaka wa kiwon lafiyar ‘yan’adam, musamman ganin cewa, tana da sinadarin fiber, haka kuma tana taimaka wa wajen rage karfin ciwon suga.

Bugu da kari, busasshiyar goruba na taimaka wa musu fama da ciwon suga da saurin narkar da abincin da mutun ya ci, haka tana dauke da sinadarin carbohydrate da kuma bitamins B.

Har ila yau, masu ilimi a fannin kiwon lafiya sun yi ittafakin cewa, goruba na taimaka wa wajen kara bunkasa aikin kwakwalwar ’yan’adam.

Goruba dai, na girma a jikin bishiya inda wasu ki ciro danyarta don su busar da ita, wasu kuma ke barinta a jikin bishiyar sai ta bushe da kanta kafin su cire ta.

Goruba
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Aure Ba Ya Ruƙuwa Sai Da Sana’a
Labarai

Aure Ba Ya Ruƙuwa Sai Da Sana’a

January 24, 2026
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC
Sana'a Sa'a

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera
Sana'a Sa'a

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera

February 1, 2025
Next Post
Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al'umma A Kagara – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.