ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

by Sadiq
4 years ago
'Yan Bindiga

Wani rahoto da kafar yada labarai ta PRNigeria ta fitar ya nuna cewa hare-haren da ake kai wa al’ummar Chonoko a jihar Kebbi, da kuma al’ummar Kagara a jihar Neja sun taimaka matuka gaya wajen raguwar kwararrun likitocin kiwon lafiya, da ayyukan ilimi, da sauran ayyukan jin kai a jihohin.

Baya ga kalubalen rashin tsaro da ake fama da shi, rahoton ya yi nuni da cewa, rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijirar ta zama abu mai wahala, ganin yadda jama’a ke matukar bukatar manyan ababen more rayuwa na dan Adam kamar abinci, ruwa, matsuguni da dai sauransu. .

  • Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane
  • Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

Sai dai kafar yada labaran ta zargi masu ruwa da tsaki a jihar da yin sama da fadi da kayan agajin da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayar ga al’ummomin da ba su da karfi.

ADVERTISEMENT

Wakilin PRNigeria, Mukhtar Madobi ne, ya bayyana hakan a yayin wani taron bita na yini biyu a Abuja mai taken: ‘Yan Jarida na Jin kai don Ci gaban Tattalin Arziki’ a lokacin da yake gabatar da wani bincike kan halin jin kai da kuma halin da ‘yan gudun hijira ke ciki a jihohin Kebbi da Neja.

Ya yi nuni da cewa ilimi wani bangare ne mai matukar muhimmanci wanda shi ma yake fama da matsalar rashin tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sakamakon binciken ya nuna cewa an rufe akasarin makarantu a kauyukan saboda fargabar hare-haren ‘yan bindiga.

“Manoma a wasu kauyukan da ke kusa da su sun koma biyan haraji ga ‘yan bindiga domin samun damar shiga gonakinsu da gudanar da ayyukan noma. Duk da haka, ayyukan noma sun ragu sosai ta yadda hakan ya haifar da karuwar matsalar karancin abinci.

“Yawancin makarantun kauyukan a rufe suke saboda fargabar hare-haren ‘yan bindiga, wanda hakan ya shafi fannin ilimi a yankin.”

Rahoton ya kara da cewa, “Yanzu haka harkar kiwon lafiya an mata kisan mummuke, saboda Babban Asibitin garin ba ya aiki yadda ya kamata saboda fargabar ‘yan bindiga.”

A halin da ake ciki, wasu asibitocin da ke cikin garuruwan an mayar da su sansanonin ‘yan gudun hijira inda ake kula da wadanda abin ya shafa.

Ya koka da yadda lamarin ya sa dalibai da dama daina zuwa makarantu, wanda hakan ya kara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yankin da ma kasar baki daya.

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Next Post
Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.