ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

by Sadiq
4 years ago
'Yan Bindiga

Wani rahoto da kafar yada labarai ta PRNigeria ta fitar ya nuna cewa hare-haren da ake kai wa al’ummar Chonoko a jihar Kebbi, da kuma al’ummar Kagara a jihar Neja sun taimaka matuka gaya wajen raguwar kwararrun likitocin kiwon lafiya, da ayyukan ilimi, da sauran ayyukan jin kai a jihohin.

Baya ga kalubalen rashin tsaro da ake fama da shi, rahoton ya yi nuni da cewa, rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijirar ta zama abu mai wahala, ganin yadda jama’a ke matukar bukatar manyan ababen more rayuwa na dan Adam kamar abinci, ruwa, matsuguni da dai sauransu. .

  • Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane
  • Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

Sai dai kafar yada labaran ta zargi masu ruwa da tsaki a jihar da yin sama da fadi da kayan agajin da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayar ga al’ummomin da ba su da karfi.

ADVERTISEMENT

Wakilin PRNigeria, Mukhtar Madobi ne, ya bayyana hakan a yayin wani taron bita na yini biyu a Abuja mai taken: ‘Yan Jarida na Jin kai don Ci gaban Tattalin Arziki’ a lokacin da yake gabatar da wani bincike kan halin jin kai da kuma halin da ‘yan gudun hijira ke ciki a jihohin Kebbi da Neja.

Ya yi nuni da cewa ilimi wani bangare ne mai matukar muhimmanci wanda shi ma yake fama da matsalar rashin tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

Sakamakon binciken ya nuna cewa an rufe akasarin makarantu a kauyukan saboda fargabar hare-haren ‘yan bindiga.

“Manoma a wasu kauyukan da ke kusa da su sun koma biyan haraji ga ‘yan bindiga domin samun damar shiga gonakinsu da gudanar da ayyukan noma. Duk da haka, ayyukan noma sun ragu sosai ta yadda hakan ya haifar da karuwar matsalar karancin abinci.

“Yawancin makarantun kauyukan a rufe suke saboda fargabar hare-haren ‘yan bindiga, wanda hakan ya shafi fannin ilimi a yankin.”

Rahoton ya kara da cewa, “Yanzu haka harkar kiwon lafiya an mata kisan mummuke, saboda Babban Asibitin garin ba ya aiki yadda ya kamata saboda fargabar ‘yan bindiga.”

A halin da ake ciki, wasu asibitocin da ke cikin garuruwan an mayar da su sansanonin ‘yan gudun hijira inda ake kula da wadanda abin ya shafa.

Ya koka da yadda lamarin ya sa dalibai da dama daina zuwa makarantu, wanda hakan ya kara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yankin da ma kasar baki daya.

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Next Post
Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.