• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Aubameyang

Pierre Emeric Aubameyang ya kammala komawa kungiyar kwallon kafa ta Olympique Marseille da ke kasar Faransa.

Dan wasan Gabon, mai shekaru 34, ya ci kwallaye uku kacal a wasanni 22 da ya buga wa Chelsea, bayan da ya koma daga Barcelona kan kudi fam miliyan 10.3 a watan Satumban da ta gabata.

  • Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2
  • Hajjin 2023: NAHCON Za Ta Kammala Dawo Da Alhazan Nijeriya A Watan Agusta

Babu wata shaida da ta bayyana ko Marseille ta biya kudin dan wasan wanda haifaffen Faransa ne.

Aubameyang ya fice daga gasar Firimiyar Ingila a karo na biyu cikin watanni 18, bayan ya shafe shekaru hudu a Arsenal daga 2018 kafin ya koma Barcelona a watan Janairun 2022.

Ya zura kwallaye 13 a wasanni 23 a cikin watanni shida da ya yi a Barcelona, amma ya kasa tabuka abin azo a gani a Stamford Bridge.

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

Gwarzon dan kwallon Afrika na 2015, ya buga wasa daya kacal a karkashin Thomas Tuchel, tsohon kocinsa a Borussia Dortmund, kafin a kore shi tare da maye gurbinsa da Graham Potter.

Kwallaye uku a wasanni uku da ya buga a watan Oktoba ya nuna yiwuwar dawowa fagen daga, amma Aubameyang ya kasa sake zura kwallo a raga.

An cire shi daga cikin ‘yan wasan da za su buga gasar zakarun Turai a gasar cin kofin zakarun Turai bayan da aka sayo sabbin ‘yan wasa a watan Janairu, ciki har da ‘yan wasan gaba Mykhailo Mudryk da Noni Madueke.

Aubameyang ya koma gasar Ligue 1 ta kasar Faransa bayan barinta shekaru 10 da suka gabata, inda ya lashe Coupe de la Ligue a 2013 a Monaco.

Aubameyang shi ne dan wasan Chelsea na bakwai da ya bar kungiyar a bana.

Dan wasan tsakiya na Croatia Mateo Kovacic ya koma Manchester City, Kai Havertz ya koma Arsenal sannan Mason Mount ya koma Manchester United, yayin da mai tsaron gida Edouard Mendy da mai tsaron baya Kalidou Koulibaly suka koma kungiyar Al-Ahli ta Saudiyya.

N’Golo Kante ya koma Saudiyya, inda ya koma Al-Ittihad, yayin da ‘yan wasan tsakiya Ruben Loftus-Cheek da Christian Pulisic suka koma AC Milan, shi kuma kyaftin din Cesar Azpilicueta ya koma Atletico Madrid.

Blues ta sayi dan wasan gaba na Brazil Angelo Gabriel, mai shekara 18 daga Santos, dan wasan Faransa Christopher Nkunku, mai shekara 25, daga RB Leipzig, da dan wasan Senegal Nicolas Jackson mai shekara 22 daga Villarreal.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid
Wasanni

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Next Post
Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.