• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
in Wasanni
0
Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Pierre Emeric Aubameyang ya kammala komawa kungiyar kwallon kafa ta Olympique Marseille da ke kasar Faransa.

Dan wasan Gabon, mai shekaru 34, ya ci kwallaye uku kacal a wasanni 22 da ya buga wa Chelsea, bayan da ya koma daga Barcelona kan kudi fam miliyan 10.3 a watan Satumban da ta gabata.

  • Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2
  • Hajjin 2023: NAHCON Za Ta Kammala Dawo Da Alhazan Nijeriya A Watan Agusta

Babu wata shaida da ta bayyana ko Marseille ta biya kudin dan wasan wanda haifaffen Faransa ne.

Aubameyang ya fice daga gasar Firimiyar Ingila a karo na biyu cikin watanni 18, bayan ya shafe shekaru hudu a Arsenal daga 2018 kafin ya koma Barcelona a watan Janairun 2022.

Ya zura kwallaye 13 a wasanni 23 a cikin watanni shida da ya yi a Barcelona, amma ya kasa tabuka abin azo a gani a Stamford Bridge.

Labarai Masu Nasaba

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Gwarzon dan kwallon Afrika na 2015, ya buga wasa daya kacal a karkashin Thomas Tuchel, tsohon kocinsa a Borussia Dortmund, kafin a kore shi tare da maye gurbinsa da Graham Potter.

Kwallaye uku a wasanni uku da ya buga a watan Oktoba ya nuna yiwuwar dawowa fagen daga, amma Aubameyang ya kasa sake zura kwallo a raga.

An cire shi daga cikin ‘yan wasan da za su buga gasar zakarun Turai a gasar cin kofin zakarun Turai bayan da aka sayo sabbin ‘yan wasa a watan Janairu, ciki har da ‘yan wasan gaba Mykhailo Mudryk da Noni Madueke.

Aubameyang ya koma gasar Ligue 1 ta kasar Faransa bayan barinta shekaru 10 da suka gabata, inda ya lashe Coupe de la Ligue a 2013 a Monaco.

Aubameyang shi ne dan wasan Chelsea na bakwai da ya bar kungiyar a bana.

Dan wasan tsakiya na Croatia Mateo Kovacic ya koma Manchester City, Kai Havertz ya koma Arsenal sannan Mason Mount ya koma Manchester United, yayin da mai tsaron gida Edouard Mendy da mai tsaron baya Kalidou Koulibaly suka koma kungiyar Al-Ahli ta Saudiyya.

N’Golo Kante ya koma Saudiyya, inda ya koma Al-Ittihad, yayin da ‘yan wasan tsakiya Ruben Loftus-Cheek da Christian Pulisic suka koma AC Milan, shi kuma kyaftin din Cesar Azpilicueta ya koma Atletico Madrid.

Blues ta sayi dan wasan gaba na Brazil Angelo Gabriel, mai shekara 18 daga Santos, dan wasan Faransa Christopher Nkunku, mai shekara 25, daga RB Leipzig, da dan wasan Senegal Nicolas Jackson mai shekara 22 daga Villarreal.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AubameyangChelseaFaransaKwallon Kafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2

Next Post

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

Related

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

2 hours ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

3 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

4 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

4 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

5 days ago
Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa
Wasanni

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

7 days ago
Next Post
Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.