• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
in Wasanni
0
Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Pierre Emeric Aubameyang ya kammala komawa kungiyar kwallon kafa ta Olympique Marseille da ke kasar Faransa.

Dan wasan Gabon, mai shekaru 34, ya ci kwallaye uku kacal a wasanni 22 da ya buga wa Chelsea, bayan da ya koma daga Barcelona kan kudi fam miliyan 10.3 a watan Satumban da ta gabata.

  • Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2
  • Hajjin 2023: NAHCON Za Ta Kammala Dawo Da Alhazan Nijeriya A Watan Agusta

Babu wata shaida da ta bayyana ko Marseille ta biya kudin dan wasan wanda haifaffen Faransa ne.

Aubameyang ya fice daga gasar Firimiyar Ingila a karo na biyu cikin watanni 18, bayan ya shafe shekaru hudu a Arsenal daga 2018 kafin ya koma Barcelona a watan Janairun 2022.

Ya zura kwallaye 13 a wasanni 23 a cikin watanni shida da ya yi a Barcelona, amma ya kasa tabuka abin azo a gani a Stamford Bridge.

Labarai Masu Nasaba

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Gwarzon dan kwallon Afrika na 2015, ya buga wasa daya kacal a karkashin Thomas Tuchel, tsohon kocinsa a Borussia Dortmund, kafin a kore shi tare da maye gurbinsa da Graham Potter.

Kwallaye uku a wasanni uku da ya buga a watan Oktoba ya nuna yiwuwar dawowa fagen daga, amma Aubameyang ya kasa sake zura kwallo a raga.

An cire shi daga cikin ‘yan wasan da za su buga gasar zakarun Turai a gasar cin kofin zakarun Turai bayan da aka sayo sabbin ‘yan wasa a watan Janairu, ciki har da ‘yan wasan gaba Mykhailo Mudryk da Noni Madueke.

Aubameyang ya koma gasar Ligue 1 ta kasar Faransa bayan barinta shekaru 10 da suka gabata, inda ya lashe Coupe de la Ligue a 2013 a Monaco.

Aubameyang shi ne dan wasan Chelsea na bakwai da ya bar kungiyar a bana.

Dan wasan tsakiya na Croatia Mateo Kovacic ya koma Manchester City, Kai Havertz ya koma Arsenal sannan Mason Mount ya koma Manchester United, yayin da mai tsaron gida Edouard Mendy da mai tsaron baya Kalidou Koulibaly suka koma kungiyar Al-Ahli ta Saudiyya.

N’Golo Kante ya koma Saudiyya, inda ya koma Al-Ittihad, yayin da ‘yan wasan tsakiya Ruben Loftus-Cheek da Christian Pulisic suka koma AC Milan, shi kuma kyaftin din Cesar Azpilicueta ya koma Atletico Madrid.

Blues ta sayi dan wasan gaba na Brazil Angelo Gabriel, mai shekara 18 daga Santos, dan wasan Faransa Christopher Nkunku, mai shekara 25, daga RB Leipzig, da dan wasan Senegal Nicolas Jackson mai shekara 22 daga Villarreal.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AubameyangChelseaFaransaKwallon Kafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2

Next Post

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

19 hours ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

22 hours ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

3 days ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

4 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

5 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

7 days ago
Next Post
Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.