ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2

by Sadiq
3 years ago
Rusau

Wata Babbar Kotun Tarayya ta bai wa Gwamnatin Kano umarnin biyan tarar naira miliyan biyu saboda yunkurin rushe wasu gine-gine.

Kotun dai ta umarci Gwamnatin Kano da ta biya wasu mutum biyu naira miliyan daya-daya saboda yunkurin rushe gine-ginensu a Unguwar Salanta da ke jihar.

  • Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau
  • Masana : Darussa Daga Shirin Kawar Da Talauci Na Kasar Sin Na Da Muhimmanci Ga Afrika

Alkalin da ya jagoranci zaman kotun a yau Juma’a, Mai Shari’a Simon Amobeda, ya ce Gwamnatin Kanon ta sauka daga kan layi ta daidai saboda shafa wa gine-gine fenti mai nuna alamar rusau kan zargin an yi su ne ba bisa ka’ida ba.

ADVERTISEMENT

Mai Shari’a Simon ya kafa hujjar cewa, Gwamnatin ta saba wa sashe na 43 da 44 da ya bai wa wadanda abin ya shafa — Saminu Shehu Muhd da Tasiu Shehu Muhammad — ’yancin mallakar gine-gine kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya tanadar.

Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, gine-gine da lamarin ya shafa sun hada da fulotai masu lamba 41 da 43 da kuma 68 a Unguwar Salanta.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Kazalika, kotun ta riki cewa kutse da Gwamnatin Kanon ta yi a gine-ginen da misalin karfe 11 na daren ranar 14 ga watan Yunin 2023 ya saba wa tanadin Kundin Tsarin Mulkin na Kasa.

Kotun ta kuma bai wa Gwamnatin Kano umarnin sake fentin gine-ginen wanda Hukumar Tsara Birni ta Kano KNUPDA ta shafa wa alamar mai dauke jan fenti.

Da yake batu bayan hukuncin, Barista Bashir Ibrahim wanda ya shigar da kara a gaban kuliya, ya bayyana hukuncin da kotun ta yanke a matsayin abun yabawa saboda kare ’yanci da martabar bilAdama.

A nasa bangaren, Lauyan Gwamnatin Kano, Barista Musa Dahuru Muhad, ya ce za su yi nazari kan hukuncin da kotun ta yanke gabanin daukar matakin da ya dace.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.