ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martabar Kasar Sin Na Karuwa A Idanun Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
Sin

Tun daga lokacin da tauraron ci gaban kasar Sin ya fara haskawa a duniya, an rika shafa wa kasar bakin fenti domin dakile ci gabanta da kuma hana ta zama mai taka muhimmiyar rawa a fagen kasa da kasa. Sai dai, sannu a hankali gaskiya na ci gaba da bayyana, inda hakan ya sa kima da martabar kasar ke karuwa a idanun duniya.

Gudunmawar Sin a fagen samar da kwanciyar hankali a duniya a bisa turbar Majalisar Dinkin Duniya, da zama kasa mafi zuba jari a bangaren makamashi mai tsafta da rage fitar da hayaki mai gurbata yanayi, da kuma huldodin kawance na bunkasa tattalin arziki da kasashe daban-daban, ta kawar da dodoridon da maha’inta ke yi.

Idan ba a manta ba, wata kididdigar da cibiyar bincike ta Pew ta fitar tare da wallafawa a watan Yulin bana, ta nuna cewa, martabar kasar Sin a idanun mutanen duniya ta karu a cikin kasashe 15 daga cikin 25 da aka yi nazari a kansu, idan aka kwatanta da bara. Kazalika, a cikin kasashe 16, an kara amincewa da hikimomi da shawarwarin da shugaba Xi Jinping ya gabatar wa duniya domin ba da gudunmawar kasar Sin ga kyautata tafiyar da harkokin duniya. Duk da cewa, ana nuna shakku a yawancin kasashe masu sukuni, amma kasashe masu tasowa da raunana na ci gaba da nuna amincewa sosai, har ma galibi suna ambaton rawar da kasar Sin take takawa a matsayin amintacciyar abokiyar tattalin arziki da kuma karuwar tasirinta a harkokin cinikayya da kayayyakin more rayuwa.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, kididdigar da aka gudanar a kan yadda ’yan kasar Sin ke kallon rawar da kasar ke takawa a duniya, watau CCGPS, wadda aka wallafa a watan Yunin 2025, ta bayyana goyon bayan al’ummar kasar mai karfi ga kara himmar kasar a fagen huldar diflomasiyya har ma da bangaren soja, tare da amfani da dabaru mafi dacewa wajen taimakawa magance kalubalen siyasar yankuna. Wannan ya nuna cewa, Sin tana tafiya a kan turbar da ta dace wajen sauke nauyinta a matsayinta na babbar kasa.

Kasashen duniya sun gaji da masu fakewa da sunan dimokuradiyya da ’yanci suna cimma boyayyun manufofinsu na haddasa yaki domin sayar da makamansu, da kakaba takunkumai masu tagayyara rayukan al’ummun kasashe, da neman yin babakere a siyasar yankuna maimakon hadin gwiwa bisa gaskiya da adalci.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Kasar Sin ba ta boye manufofinta na hulda da kasashen waje, wadanda ta kafa su a turbar hadin gwiwar moriyar juna, da zuba jari a bangaren ababen more rayuwa da kuma karfafa daukar mataki na bai-daya wajen shawo kan manyan kalubalen duniya kamar na sauyin yanayi da kuma yaki da talauci, inda take aiwatar da su a aikace ba da fatar baki ba. Su kuma masu fakewa da guzuma don su harbi karsana, mutuncinsu ya shiga “kila-wa-kala”, domin dama an ce, “mutunci madara ne, idan ya zube ba ya kwasuwa duka!” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Dajin Kainji Ne Mafakar ‘Yan Bindigar Da Ke Kai Hare-hare A Neja, Kebbi Da Kwara – Ɗan Majalisa 

Dajin Kainji Ne Mafakar 'Yan Bindigar Da Ke Kai Hare-hare A Neja, Kebbi Da Kwara - Ɗan Majalisa 

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.