ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martabar Kasar Sin Na Karuwa A Idanun Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Sin

Tun daga lokacin da tauraron ci gaban kasar Sin ya fara haskawa a duniya, an rika shafa wa kasar bakin fenti domin dakile ci gabanta da kuma hana ta zama mai taka muhimmiyar rawa a fagen kasa da kasa. Sai dai, sannu a hankali gaskiya na ci gaba da bayyana, inda hakan ya sa kima da martabar kasar ke karuwa a idanun duniya.

Gudunmawar Sin a fagen samar da kwanciyar hankali a duniya a bisa turbar Majalisar Dinkin Duniya, da zama kasa mafi zuba jari a bangaren makamashi mai tsafta da rage fitar da hayaki mai gurbata yanayi, da kuma huldodin kawance na bunkasa tattalin arziki da kasashe daban-daban, ta kawar da dodoridon da maha’inta ke yi.

Idan ba a manta ba, wata kididdigar da cibiyar bincike ta Pew ta fitar tare da wallafawa a watan Yulin bana, ta nuna cewa, martabar kasar Sin a idanun mutanen duniya ta karu a cikin kasashe 15 daga cikin 25 da aka yi nazari a kansu, idan aka kwatanta da bara. Kazalika, a cikin kasashe 16, an kara amincewa da hikimomi da shawarwarin da shugaba Xi Jinping ya gabatar wa duniya domin ba da gudunmawar kasar Sin ga kyautata tafiyar da harkokin duniya. Duk da cewa, ana nuna shakku a yawancin kasashe masu sukuni, amma kasashe masu tasowa da raunana na ci gaba da nuna amincewa sosai, har ma galibi suna ambaton rawar da kasar Sin take takawa a matsayin amintacciyar abokiyar tattalin arziki da kuma karuwar tasirinta a harkokin cinikayya da kayayyakin more rayuwa.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, kididdigar da aka gudanar a kan yadda ’yan kasar Sin ke kallon rawar da kasar ke takawa a duniya, watau CCGPS, wadda aka wallafa a watan Yunin 2025, ta bayyana goyon bayan al’ummar kasar mai karfi ga kara himmar kasar a fagen huldar diflomasiyya har ma da bangaren soja, tare da amfani da dabaru mafi dacewa wajen taimakawa magance kalubalen siyasar yankuna. Wannan ya nuna cewa, Sin tana tafiya a kan turbar da ta dace wajen sauke nauyinta a matsayinta na babbar kasa.

Kasashen duniya sun gaji da masu fakewa da sunan dimokuradiyya da ’yanci suna cimma boyayyun manufofinsu na haddasa yaki domin sayar da makamansu, da kakaba takunkumai masu tagayyara rayukan al’ummun kasashe, da neman yin babakere a siyasar yankuna maimakon hadin gwiwa bisa gaskiya da adalci.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Kasar Sin ba ta boye manufofinta na hulda da kasashen waje, wadanda ta kafa su a turbar hadin gwiwar moriyar juna, da zuba jari a bangaren ababen more rayuwa da kuma karfafa daukar mataki na bai-daya wajen shawo kan manyan kalubalen duniya kamar na sauyin yanayi da kuma yaki da talauci, inda take aiwatar da su a aikace ba da fatar baki ba. Su kuma masu fakewa da guzuma don su harbi karsana, mutuncinsu ya shiga “kila-wa-kala”, domin dama an ce, “mutunci madara ne, idan ya zube ba ya kwasuwa duka!” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Dajin Kainji Ne Mafakar ‘Yan Bindigar Da Ke Kai Hare-hare A Neja, Kebbi Da Kwara – Ɗan Majalisa 

Dajin Kainji Ne Mafakar 'Yan Bindigar Da Ke Kai Hare-hare A Neja, Kebbi Da Kwara - Ɗan Majalisa 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.