ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martabar Kasar Sin Na Karuwa A Idanun Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Sin

Tun daga lokacin da tauraron ci gaban kasar Sin ya fara haskawa a duniya, an rika shafa wa kasar bakin fenti domin dakile ci gabanta da kuma hana ta zama mai taka muhimmiyar rawa a fagen kasa da kasa. Sai dai, sannu a hankali gaskiya na ci gaba da bayyana, inda hakan ya sa kima da martabar kasar ke karuwa a idanun duniya.

Gudunmawar Sin a fagen samar da kwanciyar hankali a duniya a bisa turbar Majalisar Dinkin Duniya, da zama kasa mafi zuba jari a bangaren makamashi mai tsafta da rage fitar da hayaki mai gurbata yanayi, da kuma huldodin kawance na bunkasa tattalin arziki da kasashe daban-daban, ta kawar da dodoridon da maha’inta ke yi.

Idan ba a manta ba, wata kididdigar da cibiyar bincike ta Pew ta fitar tare da wallafawa a watan Yulin bana, ta nuna cewa, martabar kasar Sin a idanun mutanen duniya ta karu a cikin kasashe 15 daga cikin 25 da aka yi nazari a kansu, idan aka kwatanta da bara. Kazalika, a cikin kasashe 16, an kara amincewa da hikimomi da shawarwarin da shugaba Xi Jinping ya gabatar wa duniya domin ba da gudunmawar kasar Sin ga kyautata tafiyar da harkokin duniya. Duk da cewa, ana nuna shakku a yawancin kasashe masu sukuni, amma kasashe masu tasowa da raunana na ci gaba da nuna amincewa sosai, har ma galibi suna ambaton rawar da kasar Sin take takawa a matsayin amintacciyar abokiyar tattalin arziki da kuma karuwar tasirinta a harkokin cinikayya da kayayyakin more rayuwa.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, kididdigar da aka gudanar a kan yadda ’yan kasar Sin ke kallon rawar da kasar ke takawa a duniya, watau CCGPS, wadda aka wallafa a watan Yunin 2025, ta bayyana goyon bayan al’ummar kasar mai karfi ga kara himmar kasar a fagen huldar diflomasiyya har ma da bangaren soja, tare da amfani da dabaru mafi dacewa wajen taimakawa magance kalubalen siyasar yankuna. Wannan ya nuna cewa, Sin tana tafiya a kan turbar da ta dace wajen sauke nauyinta a matsayinta na babbar kasa.

Kasashen duniya sun gaji da masu fakewa da sunan dimokuradiyya da ’yanci suna cimma boyayyun manufofinsu na haddasa yaki domin sayar da makamansu, da kakaba takunkumai masu tagayyara rayukan al’ummun kasashe, da neman yin babakere a siyasar yankuna maimakon hadin gwiwa bisa gaskiya da adalci.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Kasar Sin ba ta boye manufofinta na hulda da kasashen waje, wadanda ta kafa su a turbar hadin gwiwar moriyar juna, da zuba jari a bangaren ababen more rayuwa da kuma karfafa daukar mataki na bai-daya wajen shawo kan manyan kalubalen duniya kamar na sauyin yanayi da kuma yaki da talauci, inda take aiwatar da su a aikace ba da fatar baki ba. Su kuma masu fakewa da guzuma don su harbi karsana, mutuncinsu ya shiga “kila-wa-kala”, domin dama an ce, “mutunci madara ne, idan ya zube ba ya kwasuwa duka!” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Dajin Kainji Ne Mafakar ‘Yan Bindigar Da Ke Kai Hare-hare A Neja, Kebbi Da Kwara – Ɗan Majalisa 

Dajin Kainji Ne Mafakar 'Yan Bindigar Da Ke Kai Hare-hare A Neja, Kebbi Da Kwara - Ɗan Majalisa 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.