• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maryam CTV Ta Nemi A Dinga Nuna Al’adun Bahaushe Maimakon Na Wasu Kasashen Waje A Fina-finan Kannywood

by Rabilu Sanusi Bena
10 months ago
CTV

Daya daga cikin iyaye mata da ke harkar fim wadanda kuma suka shafe shekara da shekaru a wannan masana’antar ta Kannywood ana damawa dasu Maryam Suleiman ko kuma Maryam CTV kamar yadda akafi saninta ta bayyana cewar babban abinda ke ci mata tuwo a kwarya a masana’antar Kannywood shi ne yadda ake ajiye al’adar Malam Bahaushe da dabi’unsa a cikin fina-finai a dauko wasu al’adun daban na kasashen ketare kuma duk da cewar da harshen Hausa ake amfani wajen yin fim din.

Maryam a wata hira da ta yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ ta nuna rashin jin dadinta dangane da wannan halayya ta masu daukar nauyin shirya fina-finan Hausa da kuma sauran  batutuwa da aka tabo.

  • Kyawawan Dabi’u Da Hasken Sanin Allah, Halittar Annabawa Ce Ba Koya Suke Ba
  • Jarumin Bollywood Saif Ali Khan Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Tunda farko dai Maryam ta warware zare da abawa a kan takaddamar da akeyi dangane da inda ta samo wannan suna na CTB inda ta ce ba wani abu bane ya sa ake kiranta da wannan suna illa saboda ta dade tana aiki a wannan ma’iakar Talabijin ta CTB kafin ta shigo cikin harkar Kannywood gadan-gadan.

Ta ci gaba da cewa akwai batutuwa da dama da ya kamata ace an yi duba akansu a wannan masana’anta tamu mai albarka ta Kannywood muddin ana son ci gabanta,daga ciki akwai samar da takardar yarjejeniya da ya kamata masu shirya fina-finai da jarumai za su dinga sakawa hannu a gaban shaidu dangane da abinda mai shirya fim zai biya jarumi tun kafin ma a fara aiki.

Ba wani abu ya sa nace haka ba illa saboda a tunanina wannan wata hanya ce da zata saukaka ma dukkan bangarorin biyu wato furodusa da jarumi, idan wannan abu ya tabbata zai zamana cewar akwai tsari wajen biyan kudin aiki tsakanin furodusa da jarumi don kuwa ko a addinin musulunci akwai batun yarjejeniyar kasuwanci a duk lokacin da za a kulla kasuwanci in jita.

LABARAI MASU NASABA

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

Maryam Suleiman wadda tace tun kafin a kafa wannan masana’antar ta Kannywood ta ke harkar fim ta ci gaba da cewar ni aikin nan ba bakon abu ba ne a wajena domin kuwa tun ana bani Naira 150 a matsayin albashin wata nike yin aikin wasan kwaikwayo amma yanzu sai kaga wai mutum ne zai dauke ka aiki amma ya kasa biyanka hakkinka na kudi ko bayan an kammala wannan aikin.

Hakan ya taba faruwa dani wata rana na yi wa wani furodusa aiki sai aka dauki tsawon lokaci ba tare da wannan mutumin ya biyani kudin aiki na ba, wata rana muka hadu dashi sai nike masa wasa ina cewa zan samu kudina anan Duniya ko sai mun je Lahira sai mutumin ya buda baki ya ce sai dai idan munje can Lahira sai ya bani, wannan maganar ta matukar daga mani hankali domin ban yi tunanin maganar ta fito daga bakin wannan mutumin ba.

Daga karshe ta yi kira ga jarumai musamman mata masu tasowa da su tabbatar sun koyi halaye irin na wadanda suke kallo a matsayin abin koyi a wajensu a cikin masana’antar Kannywood (Role Model), ga misali idan kina so ki zama kamar Hadiza Gabon to dole ne ki yi biyayya da jajircewa kamar yadda Hadiza Gabon ke yi hakazalika idan kinaso ki zama kamar Rahama Sadau dole ne kiyi aiki tukuru kamar yadda itama Rahama Sadau ta yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Nishadi

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Next Post
An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.