ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maryam CTV Ta Nemi A Dinga Nuna Al’adun Bahaushe Maimakon Na Wasu Kasashen Waje A Fina-finan Kannywood

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
CTV

Daya daga cikin iyaye mata da ke harkar fim wadanda kuma suka shafe shekara da shekaru a wannan masana’antar ta Kannywood ana damawa dasu Maryam Suleiman ko kuma Maryam CTV kamar yadda akafi saninta ta bayyana cewar babban abinda ke ci mata tuwo a kwarya a masana’antar Kannywood shi ne yadda ake ajiye al’adar Malam Bahaushe da dabi’unsa a cikin fina-finai a dauko wasu al’adun daban na kasashen ketare kuma duk da cewar da harshen Hausa ake amfani wajen yin fim din.

Maryam a wata hira da ta yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ ta nuna rashin jin dadinta dangane da wannan halayya ta masu daukar nauyin shirya fina-finan Hausa da kuma sauran  batutuwa da aka tabo.

  • Kyawawan Dabi’u Da Hasken Sanin Allah, Halittar Annabawa Ce Ba Koya Suke Ba
  • Jarumin Bollywood Saif Ali Khan Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Tunda farko dai Maryam ta warware zare da abawa a kan takaddamar da akeyi dangane da inda ta samo wannan suna na CTB inda ta ce ba wani abu bane ya sa ake kiranta da wannan suna illa saboda ta dade tana aiki a wannan ma’iakar Talabijin ta CTB kafin ta shigo cikin harkar Kannywood gadan-gadan.

ADVERTISEMENT

Ta ci gaba da cewa akwai batutuwa da dama da ya kamata ace an yi duba akansu a wannan masana’anta tamu mai albarka ta Kannywood muddin ana son ci gabanta,daga ciki akwai samar da takardar yarjejeniya da ya kamata masu shirya fina-finai da jarumai za su dinga sakawa hannu a gaban shaidu dangane da abinda mai shirya fim zai biya jarumi tun kafin ma a fara aiki.

Ba wani abu ya sa nace haka ba illa saboda a tunanina wannan wata hanya ce da zata saukaka ma dukkan bangarorin biyu wato furodusa da jarumi, idan wannan abu ya tabbata zai zamana cewar akwai tsari wajen biyan kudin aiki tsakanin furodusa da jarumi don kuwa ko a addinin musulunci akwai batun yarjejeniyar kasuwanci a duk lokacin da za a kulla kasuwanci in jita.

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Maryam Suleiman wadda tace tun kafin a kafa wannan masana’antar ta Kannywood ta ke harkar fim ta ci gaba da cewar ni aikin nan ba bakon abu ba ne a wajena domin kuwa tun ana bani Naira 150 a matsayin albashin wata nike yin aikin wasan kwaikwayo amma yanzu sai kaga wai mutum ne zai dauke ka aiki amma ya kasa biyanka hakkinka na kudi ko bayan an kammala wannan aikin.

Hakan ya taba faruwa dani wata rana na yi wa wani furodusa aiki sai aka dauki tsawon lokaci ba tare da wannan mutumin ya biyani kudin aiki na ba, wata rana muka hadu dashi sai nike masa wasa ina cewa zan samu kudina anan Duniya ko sai mun je Lahira sai mutumin ya buda baki ya ce sai dai idan munje can Lahira sai ya bani, wannan maganar ta matukar daga mani hankali domin ban yi tunanin maganar ta fito daga bakin wannan mutumin ba.

Daga karshe ta yi kira ga jarumai musamman mata masu tasowa da su tabbatar sun koyi halaye irin na wadanda suke kallo a matsayin abin koyi a wajensu a cikin masana’antar Kannywood (Role Model), ga misali idan kina so ki zama kamar Hadiza Gabon to dole ne ki yi biyayya da jajircewa kamar yadda Hadiza Gabon ke yi hakazalika idan kinaso ki zama kamar Rahama Sadau dole ne kiyi aiki tukuru kamar yadda itama Rahama Sadau ta yi.

CTV
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.