ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maryam CTV Ta Nemi A Dinga Nuna Al’adun Bahaushe Maimakon Na Wasu Kasashen Waje A Fina-finan Kannywood

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
CTV

Daya daga cikin iyaye mata da ke harkar fim wadanda kuma suka shafe shekara da shekaru a wannan masana’antar ta Kannywood ana damawa dasu Maryam Suleiman ko kuma Maryam CTV kamar yadda akafi saninta ta bayyana cewar babban abinda ke ci mata tuwo a kwarya a masana’antar Kannywood shi ne yadda ake ajiye al’adar Malam Bahaushe da dabi’unsa a cikin fina-finai a dauko wasu al’adun daban na kasashen ketare kuma duk da cewar da harshen Hausa ake amfani wajen yin fim din.

Maryam a wata hira da ta yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ ta nuna rashin jin dadinta dangane da wannan halayya ta masu daukar nauyin shirya fina-finan Hausa da kuma sauran  batutuwa da aka tabo.

  • Kyawawan Dabi’u Da Hasken Sanin Allah, Halittar Annabawa Ce Ba Koya Suke Ba
  • Jarumin Bollywood Saif Ali Khan Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Tunda farko dai Maryam ta warware zare da abawa a kan takaddamar da akeyi dangane da inda ta samo wannan suna na CTB inda ta ce ba wani abu bane ya sa ake kiranta da wannan suna illa saboda ta dade tana aiki a wannan ma’iakar Talabijin ta CTB kafin ta shigo cikin harkar Kannywood gadan-gadan.

ADVERTISEMENT

Ta ci gaba da cewa akwai batutuwa da dama da ya kamata ace an yi duba akansu a wannan masana’anta tamu mai albarka ta Kannywood muddin ana son ci gabanta,daga ciki akwai samar da takardar yarjejeniya da ya kamata masu shirya fina-finai da jarumai za su dinga sakawa hannu a gaban shaidu dangane da abinda mai shirya fim zai biya jarumi tun kafin ma a fara aiki.

Ba wani abu ya sa nace haka ba illa saboda a tunanina wannan wata hanya ce da zata saukaka ma dukkan bangarorin biyu wato furodusa da jarumi, idan wannan abu ya tabbata zai zamana cewar akwai tsari wajen biyan kudin aiki tsakanin furodusa da jarumi don kuwa ko a addinin musulunci akwai batun yarjejeniyar kasuwanci a duk lokacin da za a kulla kasuwanci in jita.

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Maryam Suleiman wadda tace tun kafin a kafa wannan masana’antar ta Kannywood ta ke harkar fim ta ci gaba da cewar ni aikin nan ba bakon abu ba ne a wajena domin kuwa tun ana bani Naira 150 a matsayin albashin wata nike yin aikin wasan kwaikwayo amma yanzu sai kaga wai mutum ne zai dauke ka aiki amma ya kasa biyanka hakkinka na kudi ko bayan an kammala wannan aikin.

Hakan ya taba faruwa dani wata rana na yi wa wani furodusa aiki sai aka dauki tsawon lokaci ba tare da wannan mutumin ya biyani kudin aiki na ba, wata rana muka hadu dashi sai nike masa wasa ina cewa zan samu kudina anan Duniya ko sai mun je Lahira sai mutumin ya buda baki ya ce sai dai idan munje can Lahira sai ya bani, wannan maganar ta matukar daga mani hankali domin ban yi tunanin maganar ta fito daga bakin wannan mutumin ba.

Daga karshe ta yi kira ga jarumai musamman mata masu tasowa da su tabbatar sun koyi halaye irin na wadanda suke kallo a matsayin abin koyi a wajensu a cikin masana’antar Kannywood (Role Model), ga misali idan kina so ki zama kamar Hadiza Gabon to dole ne ki yi biyayya da jajircewa kamar yadda Hadiza Gabon ke yi hakazalika idan kinaso ki zama kamar Rahama Sadau dole ne kiyi aiki tukuru kamar yadda itama Rahama Sadau ta yi.

CTV
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.