ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maryam CTV Ta Nemi A Dinga Nuna Al’adun Bahaushe Maimakon Na Wasu Kasashen Waje A Fina-finan Kannywood

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
CTV

Daya daga cikin iyaye mata da ke harkar fim wadanda kuma suka shafe shekara da shekaru a wannan masana’antar ta Kannywood ana damawa dasu Maryam Suleiman ko kuma Maryam CTV kamar yadda akafi saninta ta bayyana cewar babban abinda ke ci mata tuwo a kwarya a masana’antar Kannywood shi ne yadda ake ajiye al’adar Malam Bahaushe da dabi’unsa a cikin fina-finai a dauko wasu al’adun daban na kasashen ketare kuma duk da cewar da harshen Hausa ake amfani wajen yin fim din.

Maryam a wata hira da ta yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ ta nuna rashin jin dadinta dangane da wannan halayya ta masu daukar nauyin shirya fina-finan Hausa da kuma sauran  batutuwa da aka tabo.

  • Kyawawan Dabi’u Da Hasken Sanin Allah, Halittar Annabawa Ce Ba Koya Suke Ba
  • Jarumin Bollywood Saif Ali Khan Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Tunda farko dai Maryam ta warware zare da abawa a kan takaddamar da akeyi dangane da inda ta samo wannan suna na CTB inda ta ce ba wani abu bane ya sa ake kiranta da wannan suna illa saboda ta dade tana aiki a wannan ma’iakar Talabijin ta CTB kafin ta shigo cikin harkar Kannywood gadan-gadan.

ADVERTISEMENT

Ta ci gaba da cewa akwai batutuwa da dama da ya kamata ace an yi duba akansu a wannan masana’anta tamu mai albarka ta Kannywood muddin ana son ci gabanta,daga ciki akwai samar da takardar yarjejeniya da ya kamata masu shirya fina-finai da jarumai za su dinga sakawa hannu a gaban shaidu dangane da abinda mai shirya fim zai biya jarumi tun kafin ma a fara aiki.

Ba wani abu ya sa nace haka ba illa saboda a tunanina wannan wata hanya ce da zata saukaka ma dukkan bangarorin biyu wato furodusa da jarumi, idan wannan abu ya tabbata zai zamana cewar akwai tsari wajen biyan kudin aiki tsakanin furodusa da jarumi don kuwa ko a addinin musulunci akwai batun yarjejeniyar kasuwanci a duk lokacin da za a kulla kasuwanci in jita.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Maryam Suleiman wadda tace tun kafin a kafa wannan masana’antar ta Kannywood ta ke harkar fim ta ci gaba da cewar ni aikin nan ba bakon abu ba ne a wajena domin kuwa tun ana bani Naira 150 a matsayin albashin wata nike yin aikin wasan kwaikwayo amma yanzu sai kaga wai mutum ne zai dauke ka aiki amma ya kasa biyanka hakkinka na kudi ko bayan an kammala wannan aikin.

Hakan ya taba faruwa dani wata rana na yi wa wani furodusa aiki sai aka dauki tsawon lokaci ba tare da wannan mutumin ya biyani kudin aiki na ba, wata rana muka hadu dashi sai nike masa wasa ina cewa zan samu kudina anan Duniya ko sai mun je Lahira sai mutumin ya buda baki ya ce sai dai idan munje can Lahira sai ya bani, wannan maganar ta matukar daga mani hankali domin ban yi tunanin maganar ta fito daga bakin wannan mutumin ba.

Daga karshe ta yi kira ga jarumai musamman mata masu tasowa da su tabbatar sun koyi halaye irin na wadanda suke kallo a matsayin abin koyi a wajensu a cikin masana’antar Kannywood (Role Model), ga misali idan kina so ki zama kamar Hadiza Gabon to dole ne ki yi biyayya da jajircewa kamar yadda Hadiza Gabon ke yi hakazalika idan kinaso ki zama kamar Rahama Sadau dole ne kiyi aiki tukuru kamar yadda itama Rahama Sadau ta yi.

CTV
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za’a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
CTV
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

LABARAI MASU NASABA

CTV

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.