• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya

by Sani Anwar
1 year ago
in Labarai
0
Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkokin kiwon lafiya, sun gargadi ‘yan Nijeriya kan yin amfani da wasu kayayyakin masarufi, wadanda a hukumance ba a bayar da izinin yin amfani da su ba, ciki har da wani sinadari gishiri, wanda a yanzu haka yana iya cutar da lafiyar Dan Adam, sakamakon illar da ke tattare da shi kamar yadda Royal Ibeh ya bayyana.

Har ila yau, masana harkokin kiwon lafiyar da kwararru a kan harkar sarrafa abinci, sun yi wannan gargadi tare da jan hankulan ‘yan Nijeriya, da su zama masu lura a kan ire-iren abincin da za su kai kofar bakunansu.

  • Dan Majalisa Zai Aurar Da Mata Marayu 100 A Kebbi
  • Zaben Kano: ‘Yansanda Da Masu Zanga-zanga Sun Yi Arangama A Kano

A ‘yan kwanakin nan ne, aka samu a wasu yankunan Arewacin Nijeriya, an kai wani sinadarin gishiri; wanda a hukumance babu izinin yin amfani da ana sayarwa, inda ba tare da wani bata lokaci ba; masana suka bayar da sanarwar cewa, ba mai inganci ba ne; zai kuma iya cutarwa.

“Wannan wani sinadarin gishiri ne, mai karfin gaske da aka jima ana amfani da shi shekara da shekaru, don kara dandano da kawata girkin abinci.

Wani kwararre a kan harkar sarrafa abinci, Isah Kareem ya bayyana cewa, wajibi ne mutane su lura da irin sinadaren kayan abincin da suke amfani da su a gargajiyance, don kara dandanon abincinsu na yau da kullum, domin kauce wa fada wa hadarin cutar da lafiyarsu.

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Ya kara da cewa, “duk dadin da abinci zai yi idan aka yi amfani da ire-iren wadannan abubuwan da hukuma ba ta bayar da izinin yin amfani da su ba, a bar su ya fi alhairi domin kuwa ko shakka babu akwai hadari a tattare da su.

Sannan, ire-iren wannan gishiri, ana sayar da shi a bude ba kamar irin sauran kayan kamfani da ake adana su da kyau ba, duk da dai masu saye na rububunsa ne; saboda ganin garabasa ko arha, wanda kuma ita arha kamar yadda masu iya magana ke fada, ba ta ado.

Haka zalika, sinadarin gishirin da Hukumar NAFDAC ta amince a yi amfani da su sun hada da; Ajinomoto, Beda da sauran makamantansu, wadanda suke a cikin sacet na leda a killace ake sayar da su. Amma wadannan; wadanda ba a cikin sacet na leda suke ba, kai tsaye sun sha ban-ban da wancan.

Don haka, babu ta yadda za a iya gane alama ko wata sheda ta kamfani, ballantana a iya tabbatar da ingancinsa. Kari a kan hakan shi ne, ana sayar da shi da matukar arha; wanda duk mai hankali zai iya tabbatar da cewa, lallai wannan ba abu ne mai inganci ba, sannan kai tsaye zai iya cutarwa”.

Wata masaniya harkokin kiwon lafiyar, Foloke Ojo ta bayyana yadda a kullum ta duniya, ake kai ire-iren wadannan kayan amfanin abinci ake sayarwa, shi kuma mai saye babu abin da ke gabansa, illa dandanon da zai samu da kuma arhar abin sayarwar. Sannan, wasu ma amfani suke yi da sunayen wasu kamfanonin tare da ikirarin cewa, hajar tasu ta fi kowace haja kyau da inganci.

Ta kara da cewa, “kai ire-iren wadannan kaya tare da sayar da su a kasuwanni, ya jima da zama ruwan dare. Duk da cewa, Hukumar NAFDAC da ta SON, na bibiyar kasuwannin suna bincikawa, don bankado kayan jabu da wadanda hukuma ba ta bayar da izinin sayar da su ba”, in ji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Nijeriya Za Ta Mora Daga Taron Saudiyya Da Jamus

Next Post

Ba Na Kewar Fadar Shugaban Kasa – Buhari

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

3 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

3 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

4 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

5 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

7 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

8 hours ago
Next Post
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

Ba Na Kewar Fadar Shugaban Kasa - Buhari

LABARAI MASU NASABA

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.