• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Katagum Da Sarakunanta

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
Katagum

Masarautar Katagum tana cikin Jihar Bauchi a Tarayyar Nijeriya ne, kuma daya ce cikin masarautun da suka karbo tuta daga Shehu Usman Danfodiyo.

Masarautar a yanzu ta tashi ne daga garin Katagum in da canne ainihin tushen ta, lokacin da almajirin Shehu Usman Danfodiyo wato Malam Ibrahim Zaki ya karbo tuta ya kuma kafa masarautar,sai dai a halin da ake cikin yanzu ta dawo cikin garin Azare.

Sai dai har yanzu tana amsa sunanta na Katagum,ko da yake shi garin Katagum Hakimi ne yake iko da shi, wato Galadiman Katagum.Kuma Katagum shi ne ke zaman hedikwatar karamar hu kumar Zaki a jihar Bauchi. Sarkin Katagum da ke kan karaga shi ne Alhaji Umar Farouk, wanda ya gaji Sarkin Katagum Alhaji Dakta Muhammadu Kabir Umar CON.(1980-2017)

Azare
Azare birni ne, da ke a jihar Bauchi, a tarayyar Nijeriya.Malam Zaki ne ya kafa shi wanda kuma Shehu Usman Danfodio ya nada shi a farkon shekarar 1814.Azare hedikwatar Katagum ce a jihar Bauchi, garin Azare yana da iyaka ne daga gabas da karamar Hukumar Damban da Potiskum jihar Yobe, daga kudu kuma karamar Hukumar Misau ce,yayin da daga yamma kuma karamar Hukumar Jama’are, daga Arewa kuma ta yi iyaka da karamar hukumar Gadau a Jihar Bauchi.
An kafa garin Azare ne a shekara ta 1803 kimanin Shekaru (219) kamar yadda aka samu bayani daga iyalan Malam Lawan, mahaifin Sarakunan farko da na biyu na Azare. Malam Bonni ya kasance kanin Malam Zaki.Malam Ibrahim Zaki shi ne mazaunin garin Azare na farko, dan Malam Lawan ne wanda ya rasu a kauyen Yayu da ke kusa da Chinade.

Malam Lawan ya fara zama a garin Nafada dake cikin masarautar Gombe wanda daga baya kuma ya koma garin Yayu inda ya haifi dansa Zaki.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

Bayan rasuwar Malam Lawan, Malam Zaki ya je wurin Sheikh Usman Danfodio da ke Sakkwato domin ya karbi ragamar mulki a madadin Malam Lawan.

A shekarar 1814, Malam Zaki ya kammala makarantar Islamiyya ta Sheikh Usman Dan Fodio da ke Sakkwato, a wajen shekara ta 1809,ya fara zama a kauyen Tashena mai tazarar kilomita 9 daga Azare ta yanzu, Malam Zaki ya fara mulki ne daga 1807 zuwa 1914, sai kuma dan’uwansa ya gaje shi, wanda aka fi sani da Sulaiman Adandaya daga shekarar 1814 zuwa 1816.

Kamar yadda tarihi ya nuna, Sarkin Katagum na uku shi ne Malam Dankauwa wanda ake kallonsa a matsayin mutum mai karfin gaske. Yana da mahayan dawakai kimanin 4000 da sojoji masu kafa 20000 wadanda ya yi yaki da su da yawa kuma ya yi sarauta tsakanin 1816 zuwa 1846. A zamaninsa ne Fulani makiyaya suka yi hijira zuwa Masarautar daga sassa daban-daban na yankin Arewa.

A bayansa akwai Malam AbdurRahman wanda ke kan karagar mulki tsakanin 1846 zuwa 1851, shi ma Mallam Abdulkadir ya gaje shi daga 1851 zuwa 1868. Lokacin da Abdulkadir ya rasu a 1868, Muhammad Hajiji ya gaje shi. wanda ya hau karagar mulki tsakanin 1868 zuwa 1896. Sauran sarakunan da suka biyo bayansu sun hada da: Abdulkadir (1896-1905), Muhammadu (1947).Wani abu mai ban mamaki da ya faru a zamanin mulkin Alhaji Muhammadu shi ne, a lokacin ne aka fara samun mota ta farko a garin Azare wanda a lokacin ya kasance hedikwatar masarautar Katagum bayan da Sarkin Katagum na tara Malam AbdulKadir ya cire shi daga Katagum a shekarar 1910 domin samun saukin gudanar da mulki.
A tsakanin 1947 zuwa 1980 Masarautar Katagum ta kasance karkashin Umar Faruk inda Mallam Abubakar ya gaje shi.

An nada Alhaji Muhammadu Kabir Umar ne a shekarar 1980. Masarautar tana da wuraren tarihi, wadanda suke jan hankalin masu yawon bude ido kamar tsaunin Shira da zane-zane da mutanen farko a yankin suka yi; kabarin Malam Lawan mahaifin Malam Zaki wanda ya kafa Katagum wanda yake a garin Yayu a gundumar Chinade; katangar tsaro a kauyen Katagum da kuma kabarin Malam Zaki wanda ke wajen katangar tsaro ta Katagum.

Addini
Manyan addinai guda biyu a Azare su ne Musulunci (kimanin kashi 90) da Kiristanci (kimanin kashi 10)

Al’adu
Al’adun mutane ya fi tasiri ne da mutunta Musulunci, al’adun aure na mutane yana bisa tsarin Musulunci. Misali, neman aure da yanayin sutura.

Noma
Wuri ne da ke da kasa mai albarka domin ayyukan noma masu kyau da ake samu a yankin sun hada da gero, gyada, masara, wake,Albasa, alkama, Auduga, kayan lambu, Dogon yaro (Bishiyar Maina) da kiwo.
Azare Ita ce mafi girma a cikin garuruwan da suke kusa da yankunan da suka hada da Jama’are, Misau, Bulkachuwa, Disina, Faggo, Zadawa Madachi,da Madara.

Azare gari ne da yake da cibiyar kiwon lafiya ta tarayya, da kuma Kwalejin gwamnatin tarayya ta Azare, da kuma Kwalejin Ilimi ta Azare wadda mallakar gwamantain Jihar Bauchi ce.

Mutanen Azare yawacinsu Musulmai ne,wanda asalinsu Hausawa ne, kuma zuriyar kabilar Hausa ne. Babban aiki ko tattalin arzikin Tarihin

An samo wannan Tarihin ne daga encyclopedia ta Hausa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
majalisar kasa
Tarihi

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

August 30, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Next Post
Zirga Zirgar Jiragen Kasa Na Dakon Hajoji Tsakanin Sin Da Turai Ta Haura 90000

Zirga Zirgar Jiragen Kasa Na Dakon Hajoji Tsakanin Sin Da Turai Ta Haura 90000

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.