• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Katagum Da Sarakunanta

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Tarihi
0
Masarautar Katagum Da Sarakunanta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masarautar Katagum tana cikin Jihar Bauchi a Tarayyar Nijeriya ne, kuma daya ce cikin masarautun da suka karbo tuta daga Shehu Usman Danfodiyo.

Masarautar a yanzu ta tashi ne daga garin Katagum in da canne ainihin tushen ta, lokacin da almajirin Shehu Usman Danfodiyo wato Malam Ibrahim Zaki ya karbo tuta ya kuma kafa masarautar,sai dai a halin da ake cikin yanzu ta dawo cikin garin Azare.

Sai dai har yanzu tana amsa sunanta na Katagum,ko da yake shi garin Katagum Hakimi ne yake iko da shi, wato Galadiman Katagum.Kuma Katagum shi ne ke zaman hedikwatar karamar hu kumar Zaki a jihar Bauchi. Sarkin Katagum da ke kan karaga shi ne Alhaji Umar Farouk, wanda ya gaji Sarkin Katagum Alhaji Dakta Muhammadu Kabir Umar CON.(1980-2017)

Azare
Azare birni ne, da ke a jihar Bauchi, a tarayyar Nijeriya.Malam Zaki ne ya kafa shi wanda kuma Shehu Usman Danfodio ya nada shi a farkon shekarar 1814.Azare hedikwatar Katagum ce a jihar Bauchi, garin Azare yana da iyaka ne daga gabas da karamar Hukumar Damban da Potiskum jihar Yobe, daga kudu kuma karamar Hukumar Misau ce,yayin da daga yamma kuma karamar Hukumar Jama’are, daga Arewa kuma ta yi iyaka da karamar hukumar Gadau a Jihar Bauchi.
An kafa garin Azare ne a shekara ta 1803 kimanin Shekaru (219) kamar yadda aka samu bayani daga iyalan Malam Lawan, mahaifin Sarakunan farko da na biyu na Azare. Malam Bonni ya kasance kanin Malam Zaki.Malam Ibrahim Zaki shi ne mazaunin garin Azare na farko, dan Malam Lawan ne wanda ya rasu a kauyen Yayu da ke kusa da Chinade.

Malam Lawan ya fara zama a garin Nafada dake cikin masarautar Gombe wanda daga baya kuma ya koma garin Yayu inda ya haifi dansa Zaki.

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Bayan rasuwar Malam Lawan, Malam Zaki ya je wurin Sheikh Usman Danfodio da ke Sakkwato domin ya karbi ragamar mulki a madadin Malam Lawan.

A shekarar 1814, Malam Zaki ya kammala makarantar Islamiyya ta Sheikh Usman Dan Fodio da ke Sakkwato, a wajen shekara ta 1809,ya fara zama a kauyen Tashena mai tazarar kilomita 9 daga Azare ta yanzu, Malam Zaki ya fara mulki ne daga 1807 zuwa 1914, sai kuma dan’uwansa ya gaje shi, wanda aka fi sani da Sulaiman Adandaya daga shekarar 1814 zuwa 1816.

Kamar yadda tarihi ya nuna, Sarkin Katagum na uku shi ne Malam Dankauwa wanda ake kallonsa a matsayin mutum mai karfin gaske. Yana da mahayan dawakai kimanin 4000 da sojoji masu kafa 20000 wadanda ya yi yaki da su da yawa kuma ya yi sarauta tsakanin 1816 zuwa 1846. A zamaninsa ne Fulani makiyaya suka yi hijira zuwa Masarautar daga sassa daban-daban na yankin Arewa.

A bayansa akwai Malam AbdurRahman wanda ke kan karagar mulki tsakanin 1846 zuwa 1851, shi ma Mallam Abdulkadir ya gaje shi daga 1851 zuwa 1868. Lokacin da Abdulkadir ya rasu a 1868, Muhammad Hajiji ya gaje shi. wanda ya hau karagar mulki tsakanin 1868 zuwa 1896. Sauran sarakunan da suka biyo bayansu sun hada da: Abdulkadir (1896-1905), Muhammadu (1947).Wani abu mai ban mamaki da ya faru a zamanin mulkin Alhaji Muhammadu shi ne, a lokacin ne aka fara samun mota ta farko a garin Azare wanda a lokacin ya kasance hedikwatar masarautar Katagum bayan da Sarkin Katagum na tara Malam AbdulKadir ya cire shi daga Katagum a shekarar 1910 domin samun saukin gudanar da mulki.
A tsakanin 1947 zuwa 1980 Masarautar Katagum ta kasance karkashin Umar Faruk inda Mallam Abubakar ya gaje shi.

An nada Alhaji Muhammadu Kabir Umar ne a shekarar 1980. Masarautar tana da wuraren tarihi, wadanda suke jan hankalin masu yawon bude ido kamar tsaunin Shira da zane-zane da mutanen farko a yankin suka yi; kabarin Malam Lawan mahaifin Malam Zaki wanda ya kafa Katagum wanda yake a garin Yayu a gundumar Chinade; katangar tsaro a kauyen Katagum da kuma kabarin Malam Zaki wanda ke wajen katangar tsaro ta Katagum.

Addini
Manyan addinai guda biyu a Azare su ne Musulunci (kimanin kashi 90) da Kiristanci (kimanin kashi 10)

Al’adu
Al’adun mutane ya fi tasiri ne da mutunta Musulunci, al’adun aure na mutane yana bisa tsarin Musulunci. Misali, neman aure da yanayin sutura.

Noma
Wuri ne da ke da kasa mai albarka domin ayyukan noma masu kyau da ake samu a yankin sun hada da gero, gyada, masara, wake,Albasa, alkama, Auduga, kayan lambu, Dogon yaro (Bishiyar Maina) da kiwo.
Azare Ita ce mafi girma a cikin garuruwan da suke kusa da yankunan da suka hada da Jama’are, Misau, Bulkachuwa, Disina, Faggo, Zadawa Madachi,da Madara.

Azare gari ne da yake da cibiyar kiwon lafiya ta tarayya, da kuma Kwalejin gwamnatin tarayya ta Azare, da kuma Kwalejin Ilimi ta Azare wadda mallakar gwamantain Jihar Bauchi ce.

Mutanen Azare yawacinsu Musulmai ne,wanda asalinsu Hausawa ne, kuma zuriyar kabilar Hausa ne. Babban aiki ko tattalin arzikin Tarihin

An samo wannan Tarihin ne daga encyclopedia ta Hausa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dan fodiyoKasar HausaMasarautar Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Na Ganawar Sirri Da Abba Da Sarki Sanusi II A Fadar Kano

Next Post

Zirga Zirgar Jiragen Kasa Na Dakon Hajoji Tsakanin Sin Da Turai Ta Haura 90000

Related

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

4 days ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

2 weeks ago
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
Tarihi

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

2 months ago
Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

4 months ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

4 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

9 months ago
Next Post
Zirga Zirgar Jiragen Kasa Na Dakon Hajoji Tsakanin Sin Da Turai Ta Haura 90000

Zirga Zirgar Jiragen Kasa Na Dakon Hajoji Tsakanin Sin Da Turai Ta Haura 90000

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

July 30, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

July 30, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.