ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Katagum Da Sarakunanta

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Katagum

Masarautar Katagum tana cikin Jihar Bauchi a Tarayyar Nijeriya ne, kuma daya ce cikin masarautun da suka karbo tuta daga Shehu Usman Danfodiyo.

Masarautar a yanzu ta tashi ne daga garin Katagum in da canne ainihin tushen ta, lokacin da almajirin Shehu Usman Danfodiyo wato Malam Ibrahim Zaki ya karbo tuta ya kuma kafa masarautar,sai dai a halin da ake cikin yanzu ta dawo cikin garin Azare.

Sai dai har yanzu tana amsa sunanta na Katagum,ko da yake shi garin Katagum Hakimi ne yake iko da shi, wato Galadiman Katagum.Kuma Katagum shi ne ke zaman hedikwatar karamar hu kumar Zaki a jihar Bauchi. Sarkin Katagum da ke kan karaga shi ne Alhaji Umar Farouk, wanda ya gaji Sarkin Katagum Alhaji Dakta Muhammadu Kabir Umar CON.(1980-2017)

ADVERTISEMENT

Azare
Azare birni ne, da ke a jihar Bauchi, a tarayyar Nijeriya.Malam Zaki ne ya kafa shi wanda kuma Shehu Usman Danfodio ya nada shi a farkon shekarar 1814.Azare hedikwatar Katagum ce a jihar Bauchi, garin Azare yana da iyaka ne daga gabas da karamar Hukumar Damban da Potiskum jihar Yobe, daga kudu kuma karamar Hukumar Misau ce,yayin da daga yamma kuma karamar Hukumar Jama’are, daga Arewa kuma ta yi iyaka da karamar hukumar Gadau a Jihar Bauchi.
An kafa garin Azare ne a shekara ta 1803 kimanin Shekaru (219) kamar yadda aka samu bayani daga iyalan Malam Lawan, mahaifin Sarakunan farko da na biyu na Azare. Malam Bonni ya kasance kanin Malam Zaki.Malam Ibrahim Zaki shi ne mazaunin garin Azare na farko, dan Malam Lawan ne wanda ya rasu a kauyen Yayu da ke kusa da Chinade.

Malam Lawan ya fara zama a garin Nafada dake cikin masarautar Gombe wanda daga baya kuma ya koma garin Yayu inda ya haifi dansa Zaki.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Bayan rasuwar Malam Lawan, Malam Zaki ya je wurin Sheikh Usman Danfodio da ke Sakkwato domin ya karbi ragamar mulki a madadin Malam Lawan.

A shekarar 1814, Malam Zaki ya kammala makarantar Islamiyya ta Sheikh Usman Dan Fodio da ke Sakkwato, a wajen shekara ta 1809,ya fara zama a kauyen Tashena mai tazarar kilomita 9 daga Azare ta yanzu, Malam Zaki ya fara mulki ne daga 1807 zuwa 1914, sai kuma dan’uwansa ya gaje shi, wanda aka fi sani da Sulaiman Adandaya daga shekarar 1814 zuwa 1816.

Kamar yadda tarihi ya nuna, Sarkin Katagum na uku shi ne Malam Dankauwa wanda ake kallonsa a matsayin mutum mai karfin gaske. Yana da mahayan dawakai kimanin 4000 da sojoji masu kafa 20000 wadanda ya yi yaki da su da yawa kuma ya yi sarauta tsakanin 1816 zuwa 1846. A zamaninsa ne Fulani makiyaya suka yi hijira zuwa Masarautar daga sassa daban-daban na yankin Arewa.

A bayansa akwai Malam AbdurRahman wanda ke kan karagar mulki tsakanin 1846 zuwa 1851, shi ma Mallam Abdulkadir ya gaje shi daga 1851 zuwa 1868. Lokacin da Abdulkadir ya rasu a 1868, Muhammad Hajiji ya gaje shi. wanda ya hau karagar mulki tsakanin 1868 zuwa 1896. Sauran sarakunan da suka biyo bayansu sun hada da: Abdulkadir (1896-1905), Muhammadu (1947).Wani abu mai ban mamaki da ya faru a zamanin mulkin Alhaji Muhammadu shi ne, a lokacin ne aka fara samun mota ta farko a garin Azare wanda a lokacin ya kasance hedikwatar masarautar Katagum bayan da Sarkin Katagum na tara Malam AbdulKadir ya cire shi daga Katagum a shekarar 1910 domin samun saukin gudanar da mulki.
A tsakanin 1947 zuwa 1980 Masarautar Katagum ta kasance karkashin Umar Faruk inda Mallam Abubakar ya gaje shi.

An nada Alhaji Muhammadu Kabir Umar ne a shekarar 1980. Masarautar tana da wuraren tarihi, wadanda suke jan hankalin masu yawon bude ido kamar tsaunin Shira da zane-zane da mutanen farko a yankin suka yi; kabarin Malam Lawan mahaifin Malam Zaki wanda ya kafa Katagum wanda yake a garin Yayu a gundumar Chinade; katangar tsaro a kauyen Katagum da kuma kabarin Malam Zaki wanda ke wajen katangar tsaro ta Katagum.

Addini
Manyan addinai guda biyu a Azare su ne Musulunci (kimanin kashi 90) da Kiristanci (kimanin kashi 10)

Al’adu
Al’adun mutane ya fi tasiri ne da mutunta Musulunci, al’adun aure na mutane yana bisa tsarin Musulunci. Misali, neman aure da yanayin sutura.

Noma
Wuri ne da ke da kasa mai albarka domin ayyukan noma masu kyau da ake samu a yankin sun hada da gero, gyada, masara, wake,Albasa, alkama, Auduga, kayan lambu, Dogon yaro (Bishiyar Maina) da kiwo.
Azare Ita ce mafi girma a cikin garuruwan da suke kusa da yankunan da suka hada da Jama’are, Misau, Bulkachuwa, Disina, Faggo, Zadawa Madachi,da Madara.

Azare gari ne da yake da cibiyar kiwon lafiya ta tarayya, da kuma Kwalejin gwamnatin tarayya ta Azare, da kuma Kwalejin Ilimi ta Azare wadda mallakar gwamantain Jihar Bauchi ce.

Mutanen Azare yawacinsu Musulmai ne,wanda asalinsu Hausawa ne, kuma zuriyar kabilar Hausa ne. Babban aiki ko tattalin arzikin Tarihin

An samo wannan Tarihin ne daga encyclopedia ta Hausa

Katagum
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Zirga Zirgar Jiragen Kasa Na Dakon Hajoji Tsakanin Sin Da Turai Ta Haura 90000

Zirga Zirgar Jiragen Kasa Na Dakon Hajoji Tsakanin Sin Da Turai Ta Haura 90000

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.