• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Garkuwa Sun Buƙaci A Biya Su Fansar Miliyan 30 Kan Mutanen Da Suka Sace A Abuja

by Muhammad
1 year ago
in Al'ajabi, Labarai
0
Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, Ɗalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu garkuwa da mutane da suka yi garkuwa da wasu wasu mutum biyu a wani rukunin gidajen sojojin Nijeriya da ke birnin tarayya Abuja, sun bukaci a biya su kudin fansa miliyan N30 don su sako wadanda suka yi garkuwa da su.

LEADERSHIP ta rawaito cewa abun ya faru a daren ranar Alhamis da misalin karfe 10 na dare lokacin da masu garkuwar suka kai hari gidan Cyril Adikwu da ke rukunin gidajen sojoji a Kurudu, Abuja.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Jama’a Da Dama A Rukunin Wasu Gidaje A Abuja
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9

Adikwu, wanda ya yi nasarar guduwa a lokacin kai farmakin, ya bayyana cewa masu garkuwa da mutanen sun yi magana da shi, inda suka bukaci a biya su makudan kudin fansa cikin kayyadadden lokaci, kamar yadda Businessday ta rawaito a ranar Asabar.

“Al’amarin ya faru a daren ranar Alhamis da misalin karfe 10:00 na dare, wata mota dauke da wadanda aka yi garkuwa da su ta shiga harabar gidana, sai kwatsam masu garkuwa da mutane suka biharabayo motar zuwa cikin harabar,” in ji Adikwu.

“Kusan su takwas ne, kuma sun bi ta hanyar daji da ke kan tudu zuwa wancan wurin, an kira ni ne domin in bayar da kudin fansa, ba na son na ambaci adadinsu, domin tuni bayanan karya ya cika ko’ina a kafafen yada labarai. duk abin da ya faru, amma ina tabbatar muku sun bukaci fiye da miliyan 30.”

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, lamarin yin garkuwa da mutane a Abuja ba wani abu ba ne sabo. Ko a makon da ya gabata, ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane akalla 10 a unguwar Dutse-Alhaji da ke babban birnin tarayya Abuja, bayan da aka ce wasu ‘yan bindiga sanye da kayan sojoji sun mamaye yankin.

Masu garkuwa da mutane sanye da kaya irin na makiyaya, an ce sun mamaye gidan ne da yamma da misalin karfe 7:30 na dare.

Wannan lamari dai na zuwa kwanaki kadan bayan da wasu ‘yan bindiga suka kashe wata budurwa mai suna Nabeeha Al-Kadriyar da suka yi garkuwa da ita da wasu mata guda biyar a birnin na Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaGarkuwaKudin Fansa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karatun `Ya`ya Mata A Wannan Zamanin

Next Post

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?

Related

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

37 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

2 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

5 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

6 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

7 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

8 hours ago
Next Post
Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.