• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Garkuwa Sun Buƙaci A Biya Su Fansar Miliyan 30 Kan Mutanen Da Suka Sace A Abuja

by Muhammad
1 year ago
in Al'ajabi, Labarai
0
Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, Ɗalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu garkuwa da mutane da suka yi garkuwa da wasu wasu mutum biyu a wani rukunin gidajen sojojin Nijeriya da ke birnin tarayya Abuja, sun bukaci a biya su kudin fansa miliyan N30 don su sako wadanda suka yi garkuwa da su.

LEADERSHIP ta rawaito cewa abun ya faru a daren ranar Alhamis da misalin karfe 10 na dare lokacin da masu garkuwar suka kai hari gidan Cyril Adikwu da ke rukunin gidajen sojoji a Kurudu, Abuja.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Jama’a Da Dama A Rukunin Wasu Gidaje A Abuja
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9

Adikwu, wanda ya yi nasarar guduwa a lokacin kai farmakin, ya bayyana cewa masu garkuwa da mutanen sun yi magana da shi, inda suka bukaci a biya su makudan kudin fansa cikin kayyadadden lokaci, kamar yadda Businessday ta rawaito a ranar Asabar.

“Al’amarin ya faru a daren ranar Alhamis da misalin karfe 10:00 na dare, wata mota dauke da wadanda aka yi garkuwa da su ta shiga harabar gidana, sai kwatsam masu garkuwa da mutane suka biharabayo motar zuwa cikin harabar,” in ji Adikwu.

“Kusan su takwas ne, kuma sun bi ta hanyar daji da ke kan tudu zuwa wancan wurin, an kira ni ne domin in bayar da kudin fansa, ba na son na ambaci adadinsu, domin tuni bayanan karya ya cika ko’ina a kafafen yada labarai. duk abin da ya faru, amma ina tabbatar muku sun bukaci fiye da miliyan 30.”

Labarai Masu Nasaba

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, lamarin yin garkuwa da mutane a Abuja ba wani abu ba ne sabo. Ko a makon da ya gabata, ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane akalla 10 a unguwar Dutse-Alhaji da ke babban birnin tarayya Abuja, bayan da aka ce wasu ‘yan bindiga sanye da kayan sojoji sun mamaye yankin.

Masu garkuwa da mutane sanye da kaya irin na makiyaya, an ce sun mamaye gidan ne da yamma da misalin karfe 7:30 na dare.

Wannan lamari dai na zuwa kwanaki kadan bayan da wasu ‘yan bindiga suka kashe wata budurwa mai suna Nabeeha Al-Kadriyar da suka yi garkuwa da ita da wasu mata guda biyar a birnin na Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaGarkuwaKudin Fansa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karatun `Ya`ya Mata A Wannan Zamanin

Next Post

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?

Related

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

31 minutes ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

3 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

4 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

5 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

6 hours ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

14 hours ago
Next Post
Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.