• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Zanga-Zanga A Kano Na Neman Taimakon Ƙasar Rasha

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
in Tsaro
0
Masu Zanga-Zanga A Kano Na Neman Taimakon Ƙasar Rasha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Asabar, masu zanga-zanga a jihar Kano sun nemi shugaban ƙasar Rasha, Vladimir Putin, ya sa baki, suna daga tutar Rasha a bisa fusatar rashin kulawa da koke-kokensu daga gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu. Wannan ya faru ne a rana ta uku ta zanga-zangar tsadar rayuwa wato #EndBadGovernance da aka yi kan tsananin yunwa da talauci a Najeriya.

Zanga-zangar ta rikiɗe ta zama tashin hankali, inda ta haifar da rikici tsakanin wasu ‘yan daba da jami’an tsaro, wanda ya janyo mutuwar mutane da dama da raunata wasu.

  • Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
  • Tsadar Rayuwa: Atiku Ya Yi Allah Wadai Da Harbin Masu Zanga-zanga 

Shaidu sun ruwaito cewa rikicin ya fara ne lokacin da matasa suka saɓa dokar hana fita da jihar ta ƙaƙaba don ci gaba da zanga-zangar a yankunan Rijiyar Lemo, da Kurna zuwa Bachirawa, da Kofar Nasarawa, da Unguwa Uku.

Abdulkadir Musa, mazaunin Rijiyar Lemo, ya bayyana cewa an harbe a ƙalla mutane takwas, ciki har da mata da yara, tare da tabbatar da mutuwar tsohuwa da wasu mutane uku. An ce ƴan dabar sun yi ƙoƙarin fasa shaguna suna fakewa da zanga-zangar yunwa, wanda ya haifar da ƙarin tashin hankali da raunuka.

Masu amfani da kafofin sada zumunta sun yi wallafe wallafe game da tarzomar, suna nuna yadda ƴansanda suka yi amfani da ƙarfi don tarwatsa masu zanga-zangar.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 3, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace

‘Yansandan Sun Kama Wanda ake Zargi Da Satar Mutane A Sokoto

Rundunar Ƴansanda ta jihar Kano ba ta yi ƙarin haske kan rahotannin kisan ba, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta. Ƙoƙarin tuntubar mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, bai yi nasara ba saboda ba a iya samun sa ta waya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Inganta Sassan Ba Da Hidima

Next Post

Jami’in Zimbabwe Ya Yabawa Kamfanin Kasar Sin Da Ya Goyi Bayan Ajandar Bunkasa Masana’antun SADC

Related

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 3, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace
Tsaro

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 3, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace

5 days ago
Ana Zargin Wani Ɗansanda Da Kisan Wata Mata Kan Cin Hancin Naira 2,000 — Bincike
Tsaro

‘Yansandan Sun Kama Wanda ake Zargi Da Satar Mutane A Sokoto

5 days ago
Dole Jama’a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda
Tsaro

Dole Jama’a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

7 days ago
Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara
Tsaro

Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara

2 weeks ago
Sojojin Nijeriya Sun Yi Lugudan Wuta Kan Sansanin Ƴan Ta’adda A Borno
Tsaro

Sojojin Nijeriya Sun Yi Lugudan Wuta Kan Sansanin Ƴan Ta’adda A Borno

3 weeks ago
Kicibus: An Gabza Yaki Tsakanin Yan Bijilanti Da ‘Yan Fashi, Sun Kashe Barayi 30 A Zamfara
Tsaro

Kicibus: An Gabza Yaki Tsakanin Yan Bijilanti Da ‘Yan Fashi, Sun Kashe Barayi 30 A Zamfara

1 month ago
Next Post
Jami’in Zimbabwe Ya Yabawa Kamfanin Kasar Sin Da Ya Goyi Bayan Ajandar Bunkasa Masana’antun SADC

Jami’in Zimbabwe Ya Yabawa Kamfanin Kasar Sin Da Ya Goyi Bayan Ajandar Bunkasa Masana’antun SADC

LABARAI MASU NASABA

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.