• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
8 months ago
in Adon Gari
0
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zahra’u Adam Matashiya ce mai hazaka da jajircewa kan neman ilimi, inda ta shawarci mata da su dage da karatu domin a cewarta idan mata suka yi karatu za su taimakawa kansu da ‘ya’yansu, baya ga haka ta bayyana wa wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM, irin nasarori da kalubalen da ta fuskanta, kamar dai yadda za ku karanta kamar haka:

 

Da farko za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Sunana Zara’u Adamu Sulaiman, an haife ni a garin Hadejia, na yi primary da sikandire a Usman bin Affan, kuma na yi sikandire a GGDSS Hadejia yanzu ina NCE a College Of Education Legel Studies.

 

Labarai Masu Nasaba

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Zara’u kina da aure ce?

A a bani da aure

 

Malama Zara’u kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa gaba?

A’a gaskiya kasancewar ni daliba ce, gaskiya ni ba ni da wata sana’a, sai dai karatu, shi na sa a gaba, tukunnan sana’a, sai mun kammala karatu in sha Allahu.

 

Me kike karanta?

Ina karantar fannin Tattalin Arziki da Turanci

 

Me yaja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun wadannan fannoni?

Saboda ina da sha’awar sanin harkokin kasa ciki da waje, sannan in san yadda ake tattalin arzikin kasa da na gida musamman ma ina ganin ni mace ce da zan rike gida.

Idan na iya tattala kayan gida, na iya adana su ba’a almabozarancin su, to ina ganin wannan ma yana da kyau.

Sannan idan na karanci tattali zan san abubuwan da suka shafi kasa, abubuwan da ya kama a yi a kasa da wanda bai kamata ba. Za ka gane yadda ake lafiyar da kasar ya yi daidai ko bai yi ba.

 

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin karatunki?

Zngon karatuna na biyu, a matakin karatuna na uku na fiuskanci kalubale da dama, wanda sai dai na yi addau’a da fatan kada na sake samun irin wannan abin, Allah ya kiyaye mana gaba.

 

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

To Alhamdulillah ka ga komai naka yana tafiya yadda ya kamata, karatun na babu wata matsala, to wannan ba karamar nasara bace a wajena, gashi yanzu har mun kawo shekara ta karshe, muna zango na karshe kwanaki kadai ya rage mu kammala ai sai dai na ce Alhamdulillah.

 

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da yafi faranta min rai game da karatuna, shi ne na shiga jarabawa na ga na gane kowace tambaya, a gasukiya wannan ba karamin jin dadi nake ba, yana farantamin rai sosai.

 

Dame kike so mutane su rika tunawa dake?

Ina so mutane su rinka tunawa da ni akan hakuri na da son zaman Lafiya.

 

Wanne irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

A ce Allah ya yi min albarka ya kuma jikan mahaifana a gaskiya ina jin dadin wannan addu’ar sosai kuma tana birge ni.

 

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Ina samun goyon baya daga wajen iyaye na sosai da sosai, saboda su ke karfafa min gwiwa wajen na jajirce akan karatu na, kuma su suka saka ni a makaranta tun ina karama har na kawo yanzu, to babu abin da zan ce da su sai godiya, ina gode wa Allah Alhamdulillah, sannan ina gode wa iyayena sosai.

 

Kawaye fa?

Kawata daya ce mai suna zaliha, muna tare da ita muna karatu.

 

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Cikin kayan sawa ina son dogowar riga ta yadi, kayan kwalliya kuma gaskiya ni ba ma’abociyar kwalliya bace.

 

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Shawarata a gareku ‘yan uwana mata ku dage da karatu domin tallafawa rayuwarku da ta ‘ya’yanku


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wike Ya Bai Wa Asibitocin Gwamnati Umarnin Tallafa Wa Wadanda Turmutsitsin Abuja Ya Rutsa

Next Post

Babban Aikin “Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana A Wajen Da Ake Kiwon Kifi” A Sin Ya Fara Aiki

Related

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

3 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

4 weeks ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

3 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

4 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

6 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

7 months ago
Next Post
Babban Aikin “Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana A Wajen Da Ake Kiwon Kifi” A Sin Ya Fara Aiki

Babban Aikin “Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana A Wajen Da Ake Kiwon Kifi” A Sin Ya Fara Aiki

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

August 22, 2025
Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

August 22, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

August 22, 2025
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

August 22, 2025
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

August 22, 2025
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.