• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Da Ake Dauka Don Kauce Wa Karancin Abinci A Nijeriya –Ministar Jin Kai

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Rahotonni
0
Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram
  •  Shugaba Buhari Ya Sa A Raba Tirelar Abinci 400
  • Ba Cikin Dare Ko A Rami Muke Rabo Ba, Kowa Na Gani
  •  Zargin Da Gwamnan Benuwai Ya Yi Ba Gaskiya Ba Ne
  • Allah Ya Wanke Mu Daga Zargin Boye Tallafin Korona

Ambaliyar Ruwan da ta auku a daminar da ta gabata ta 2022 ta haifar da barna mai dimbin yawa a Nijeriya inda aka yi kiyasin cewa ta shafi akalla mutum miliyan uku da dubu dari biyu da shatara da dari bakwai da tamanin, inda sama da miliyan daya kuma suka rasa muhallansu baya ga gonakai sama da hekta dubu biyar da al’amarin ya shafa da sauran asarori daba-daban.

Yanzu haka dai ma’aikatar kula da al’amuran jin kai ta kasa ta dukufa rabon kayan tallafi ga wadanda abin ya shafa. MINISTAR JIN KAI, HAJIYA SADIYA FAROUK ta yi wa wakilinmu na fadar shugaban kasa, JONATHAN INDA-ISAIAH bayani a kan tallafin da ake yi da matakan da aka dauka na magance karincin abinci a Nijeriya sakamakon ambaliyar da kuma hanyoyin da ma’aikatar ke bi wajen ganin ba a maimaita handama da babakere na kayan tallafin ba kamar yadda aka gani lokacin rabon tallafin Korona. Ga dai yadda hirar tasu ta kasance kamar yadda RABI’U ALI INDABAWA ya rubuta:

Ambaliyar ruwa kusan ta auku a kowace kusurwa ta kasar nan, ko za ki bayyana wa masu karatu ayyukan jin kai da kuke yi?

Kamar yadda ka sani wannan ambaliya ta faru tsakanin wannan watan da ya wuce, watan Satumba da karshe zuwa Oktoba, kuma garuruwa da dama a fadin kasar nan wannan ambaliya ta shafe su, mun zo mun ba da bayani kan abin da gwamnatin tarayya ta yi na magancewa da ganin an kawo sassauci ga wannan abu da ya faru, saboda ambaliya ta zo wa mutane da yawa, jama’a sun rasa gonakinsu wasu ma sun rasa rayukansu, wasu kuma sun rasa hanyar cin abincinsu.

Gwanatin Tarayya a karkashin ma’aikatata ta ba da tallafin agaji ga wadanda abin ya shafa, wannan shi ne abin da muka zo muka fada muku masu yada labarai don ku san abin da muke yi a gwamnatance.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

Akwai tsoro da ake cewa wannan ambaliya za ta haifar da karancin abinci, ko me kuke yi a gwamnatance?
Abin da muke yi a yanzu shi ne, muna zuwa daukar alkaluma don mu ga iya yadda yawan abin yake, kuma a zauna a fidda manufofi daban-daban na ganin ba a kai ga wannan hali na karancin abinci ba, kamar yadda ka sani, akwai noman rani da za a yi wanda shi ne za mu ba da muhimmanci a kai kwarai da gaske a ga cewa an taimaka wa manoma an tallafa musu domin su yi noman rani ko ina a kasar nan.

Akwai bayanai da kuka yi wa mutane na cewa su lura da abin da ya faru kafin aukuwarsa?
An yi bayanai da dama babu iyaka ta kowane fanni, kafofin yada labarai daban-daban, mun isar da shi a gwamnatance, mun isar a al’umance, mun isar da shi a kungiyance, a ma’aikatata da ma’aikatar samar da albarkatun ruwa, da kuma ta masu sanin yanayi, su ma sun fitar da wannan kashedin, cewa wannan abu zai faru a wadannan jihohi kuma ga abin da zai biyo baya, to amma ga yadda lamarin yake, wasu sun ji wasu basu ji ba, abin bakin ciki har wasu mutane sun rasa rayukansu bisa wannan.

Amma fa kamar yadda ka sani ita ambaliya ba aba ce wadda za a iya hanawa ba, in dai za ta zo, to dole za ta zo. Abin da yake muhimmi shi ne a dauki matakan da ya kamata a dauka domin a samu sassauci ga faruwarta ya zama idan ta zo ba za ta tafi da rayuka ba kamar yadda muka gani, kuma wadanda ya kamata su yi abin da ya kamata, su yi.

Lokacin Korona mun ga yadda ma’aikatarki ta rika ba da tallafi, amma kuma sai aka samu wasu bata-gari suka rika almundahana da akai, a wannan lokaci wane mataki kuka dauka wajen ganin abin da kuka bayar ya isa hannun talakawa ba tare da ana cin dunduniyarku ba?
Gaskiya kam mun dauki matakai koacin Koronan nan duk da Allah ya wanke mu daga baya amma dai ba za mu so irinsa ya kara faruwa ba.

Matakin da muka dauka na farko shi ne, mun je mun fitar da kungiyoyi a kowace jiha da suka hada da kungiyoyin addini da kungiyoyi masu zaman kansu da kungiyoyin al’umma, da Red Cross, duka aka rubuta musu cewa za mu zo wannan jiha kuma ga kayan abincin da za mu kawo kuma ga kayan tallafin da za mu kawo, kuma za mu kawo wa mutum kaza, to wannan ya magance kuma ina ganin zai ci gaba da magance irin wannan abin da ya faru a baya a ga cewa duk abin da aka tura ya isa ga wadanda ake nufi a kan idon kowa kuma a kan idon mutanen da aka ce za a ba wa wannan taimako.

Kayan tallafin da aka raba ya kai Tan nawa?
To kamar yadda muka fada, shugaban kasa ya ba da umarnin cewa ma’aikatar gona ta ba mu abincin da yake rumbu kamar Tirela 400 kenan na kayan abinci wanda kuma mun raba shi kuma muna cikin rabawa. Sannan ban da wadansu kayan abincin da ma’aikatar NEMA ta saya, sannan kuma akwai kayan ma da ba na abinci ba kamar kayan shimfida da sauran kayan rayuwa na yau da kullum.

Gwamnan Benuwai yana ta korafin cewa gwmanti ba ta taimaka masa ba, ko za ki yi bayani a kan wannan?
To Jihara Beniwe dai kam ba karamin taimako muka ba wa jihar ba, duka ma’aikatun da ke karkashin ma’aikatata kafin ma ambliyar ruwan nan mun kai taimako Jihar Beniwai. Beniwai tana cikin jihohin da NEMA ta kai wa abin da ake cewa (Freefair), su aka fara kai wa a duk fadin kasar nan da suke amfani da shi wanda yanzu ake tunanin a kai wasu ma jihohin Kudu. To abin da muke yi ba cikin dare muke yi ko cikin rami ba kowa yana gani, kuma muna ajiye dukkanin bayanai, wannan ba Beniwai ba ne kadai ba duk inda abu ya faru muna kai taimako.

Ana siyasantar da wannan abin, wasu gwamnoni suna ganin kamar ba a yi komai ba, ku ma kuna kallon siyasar?
Aikinmu ba na siyasa ba ne, aikinmu na taimakon Dan’adam ne ga wanda Ibtila’i ya afka masa mu taimaka masa, ma’aikatarmu sunanta Ma’aikatar Ba Da Agajin Gaggawa da Jin Kai, abin da ban mamaki manya su fito suna cewa haka amma mun yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bagudu Ya Amince Da Nadin Sarakunan Gargajiya 2 A Masarautar Yauri Ta Jihar Kebbi

Next Post

PDP Ce Kaɗai Mai Karsashin Lashe Zaɓe – Atiku

Related

Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

6 days ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

6 days ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

2 weeks ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2 weeks ago
Next Post
PDP Ce Kaɗai Mai Karsashin Lashe Zaɓe – Atiku

PDP Ce Kaɗai Mai Karsashin Lashe Zaɓe - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

July 24, 2025
Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

July 24, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

July 24, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

July 24, 2025
Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

July 24, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

July 24, 2025
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

July 24, 2025
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

July 24, 2025
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

July 24, 2025
Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

July 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.