• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Kasashen Ketare
0
Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Umm Hudaifa, matar shugaban kungiyar IS Abu Bakr al-Baghdadi, na zaman gidan yari yanzu a Iraki, matar marigayi shugaban kungiyar Islamic State ta ba da labarin rayuwarta. Umm Hudaifa ce matar Abu Bakr al-Baghdadi ta farko kuma ta shaida lokacin da ya mulki bangarorin Syriya da Iraki a matsayin Daular Musulunci. Yanzu tana tsare a wani gidan yarin Iraki inda ake tuhumar ta da laifukan ta’addanci.

A bazarar shekarar 2014, Umm Hudaifa na zaune a Birnin Rakka, garin Syriya kenan da IS ta fi karfi a lokacin, tare da mijinta.

  • Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano
  • Asibitin Yariman Bakura Ya Fara Amfana Da Dokar Ta-ɓaci A Sashen Kiwon Lafiyar Zamfara

Yayin da jagoran da ake nema ruwa a jallo ke boye-boye a wurare daban-daban, a wannan lokacin ne ya tura dakaru su kwaso ‘ya’yanta biyu kanana. “Ya fada min cewa zai kai yaran ne don koya musu ninkaya a ruwa,” in ji Umma Hudaifa.

Akwai boyayyar talabijin da take amfani da ita a asirce.

Ina kunna ta idan ba ya gidan,” a cewarta ya zaci ba ta aiki. Ta kara da cewa an kebance ta daga sauran duniya ta hanyar hana ta amfani da duk wata na’ura kamar waya da kuma kallon talabijin tun daga shekarar 2007.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

‘Yan kwanaki bayan daukar yaran, ta ce ta sha mamaki da ta kunna talabijin din ta ga mijinta na yi wa jama’a jawabi a babban masallacin al-Nuri da ke Birnin Mosul na Iraki ya na bayyana kansa karon farko a matsayin shugaban Daular Musulunci.

Yulin 2014

An ga bidiyon al-Baghdadi yana neman hadin kan Musulmai a matsayin shugabansu a duka fadin duniya sanye da bakaken kaya, wanda shi ne lokaci mafi girma a rayuwar kungiyar IS yayin da ta mamaye wasu yankunan Iraki da Syriya.

Umm Hudaifa ta ce ta kadu da gano cewa ‘ya’yanta suna Mosul tare da shi – ba wajen koyon ninkaya ba.

Mun samu wuri a wani dakin karatu inda muka yi magana tsawon awa biyu.

Yayin tattaunawar ta nuna cewa ita aka zalinta bayan ta yi yunkurin guduwa daga hannun mijin nata kuma ta musanta hannu a duk wasu ayyukan IS na rashin imani.

Hakan ya saba sosai da yadda aka bayyana ta a takardun kotu da aka shigar da karar da al’ummar Yazidi suka shigar, wadanda ‘yan IS suka yi garkuwa da su kuma suka yi musu fyade, sun zarge ta da hada baki wajen mayar da su bayi.

Ba ta daga kanta ba yayin hirar, ko sau daya. Tana sanye da bakaken kaya kuma wani bangare na fuskarta kawai ake gani, daga hancinta zuwa kasa.

An haifi Umm Hudaifa a 1976 a Iraki kuma ta auri Ibrahim Awad al-Badri, wanda daga baya aka sani da Abu Bakr al-Baghdadi a shekarar 1999.

Ya karanci fannin harkokin Shari’ar Musulunci a Jami’ar Baghdad kuma ta ce a lokacin yana da bin addini amma ba mai tsattsauran ra’ayi ba ne.

Sai kuma a 2004, shekara daya bayan Amurka ta jagoranci mamaye Iraki, dakarun Amurka suka tsare al-Baghdadi a sansanin Bucca da ke Kudancin kasar tare da wasu mazajen, wadanda daga baya suka zama jagororin IS.

Bayan sakinsa, ya yi ikirarin cewa ya sauya: “Ya koma mara fushi kuma ya daina yi wa mutane tsawa cikin fushi.”

Wasu da suka san shi sun ce ya fara hulda da al-Ka’ida ne kafin ya je sansanin Bucca, amma a cewarta daga wannan lokacin ne ya koma mai tsattsauran ra’ayi. “Ya fara samun matsala a tunaninsa,” in ji ta. Da aka tambaye ta dalili, sai ta ce “ya ga wasu abubuwa da ba za ku gane ba”.

Tana ganin duk da bai fada mata ba, amma “lokacin da ake tsare da shi an ci zarafinsa ta hanyar lalata”. Wasu hotuna da suka bulla na gidan yarin da Amurka ke jagoranta a Iraki mai suna Abu Ghraib sun nuna yadda ake tilasta wa fursunoni tayar wa da mutane sha’awa da kuma saka su yin wasu abubuwa na kaskanci.

Mun fada wa Ma’aikatar Tsaro ta Amurka zarge-zargen da ta yi amma ba ta ba da wata amsa ba.

Ta ce ta fara mamakin ko ya shiga wata kungiyar gwagwarmaya ne. “Na sha caje kayansa idan ya dawo gida, ko idan yana wanka ko kuma idan yana barci.

“Har jikinsa nake dubawa ko zan ga wani rauni, na yi mamaki,” a cewarta, amma ba ta ga komai ba.

“Na fada masa cewa, ‘Ka shiga hanyar bata, abin ya bata masa rai.”

Ta fadi yadda suke yawan sauya gidan zama, da yadda suka samu takardun bogi na karya, da yadda ya auri mace ta biyu. Umm Hudaifa ta ce ta nemi ya sake ta amma kuma ba za ta iya yarda da sharadin da ya ke gindaya mata ba, na cewar sai dai ta bar masa ‘ya’yanta, wanda hakan ya sa dole ta ci gaba da zama da shi a hakan.

Yayin da Iraki ta fada rikicin kungiyoyi da ya kai har 2008, ta san cewa lallai akwai hannunsa a bangaren kungiyoyin masu ikirarin jihadi na Sunni. A 2010 ya zama shugaban kungiyar Islamic State ta Iraki – bayan kafa ta a 2006, wata gamayya ce ta kungiyoyi masu ikirarin jihadi a Iraki.

“Mun koma Idlib a Syria a watan Janairun 2012, kuma a nan ne na fahimci cewa shi ne Khalifa,” in ji Umm Hudaifa.

Kungiyar Islamic State ta Iraki ta hade daga baya don kafa babbar Islamic State.

A lokacin, ta ce sai ya fara saka irin tufafin ‘yan Afghanistan, ya tara gemmu kuma ya fara daukar karamar bindiga.

Bayan lamarin tsaro ya tabarbare a Arewa maso Yammacin Syriya, sai suka koma Birnin Rakka, wanda daga baya IS ta mayar da shi babban birnin daularta.

Tuni aka san irin rashin imanin kungiyoyin da suka hadu suka zama IS, amma a 2014 da 2015 abin ya kara fitowa fili. Wata tawagar Majalisar Dinkin Duniya ta gano cewa IS ta aikata kisan kare-dangi a kan al’ummar Yazidi marasa rinjaye.

IS kan yada rashin imaninta ta bidiyo. Ta kashe kusan mutum 1,700 wanda akasarinsu dakarun ‘yan Shi’a ne, yayin da suke dawowa daga wani sansani a Arewacin Bagadaza.

Sauran sun kunshi kona wani matukin jirgin sama dan kasar Jordan.

Wasu matan da suka zauna ‘yan IS yanzu na cewa ba su san yadda abin yake ba a lokacin, shi ya sa na matsa wa Umm Hudaifa kan ra’ayinta game da lokacin, ta ce ko a lokacin ba ta iya kallon hotunan rashin imanin saboda “zubar da jini haka kawai rashin imani ne kuma yin hakan keta alfarmar dan’adam ne”.

Umm Hudaifa ta ce ta kalubalanci mijinta game da “jinin mutanen da babu ruwansu” da ya zubar kuma ta fada masa “akwai abubuwan da za su iya yi kamar yadda Shari’ar Musuluncin ta tanada, kamar dora su kan hanyar tuba”.

Ta ce ya kan boye kwamfutarsa a cikin wata jaka. “Na yi kokarin shiga na ga abin da ke faruwa amma ba ni da ilimin kimiyya, kuma ko da yaushe kwamfutr sai ta tambaye ni kalmomin sirri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ISISMataSirri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya

Next Post

Hajji 2024: Sarki Salman Na Saudiyya Ya Bai Wa Mahajjata Kyautar Al-ƙur’ani Mai Girma

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

3 days ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

4 days ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

1 week ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

2 weeks ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
Hajji 2024: Sarki Salman Na Saudiyya Ya Bai Wa Mahajjata Kyautar Al-ƙur’ani Mai Girma

Hajji 2024: Sarki Salman Na Saudiyya Ya Bai Wa Mahajjata Kyautar Al-ƙur'ani Mai Girma

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

May 17, 2025
Me Ya Sa Manchester United Ta Fi Yin Kokari A Europa League?

Me Ya Sa Manchester United Ta Fi Yin Kokari A Europa League?

May 17, 2025
Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

May 17, 2025
Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

May 17, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

May 17, 2025
Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

May 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

May 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

May 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.