ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asibitin Yariman Bakura Ya Fara Amfana Da Dokar Ta-ɓaci A Sashen Kiwon Lafiyar Zamfara

by Leadership Hausa
2 years ago
asibiti

Asibitin Yariman Bakura da ke Gusau ya fara amfana da dokar ta-ɓaci a sashen kiwon lafiya da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ayyana sakamakon ƙaddamar da aikin gyara, ingantawa da kuma samar da kayan aiki a asibitin ƙwararrun ɗaya tilo mallakar gwamnatin jihar.

An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a ranar Alhamis da ta gabata a asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura da ke Gusau, babban birnin jihar.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa ingantawar za ta mayar da asibitin zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

A yayin jawabinsa a wurin taron, Gwamna Lawal ya tabbatar da cewa, gyaran zai inganta tsarin kula da marasa lafiya ta musamman, da ƙara yawan ma’aikatan kiwon lafiya, da kuma inganta tsarin ayyukan, wanda zai haifar da ingantaccen kiwon lafiya.

“Mun zo nan a yau ne domin ƙaddamar da gyare-gyare da kuma samar da kayan aiki na asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura da ke Gusau. Aikin zai kuma ƙunshi samar da kayan aikin jinya ga asibitin. Wannan aiki dai ya biyo bayan ayyana dokar ta-ɓaci ne a fannin kiwon lafiyar jihar, bayan na ilimi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

“Wannan babban ƙalubale ne da muka gada a wannan fanni lokacin da muka karɓi ragamar mulkin jihar.

“Asibitin na cikin mawuyacin hali duk da irin rawar da yake takawa wajen samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga mazauna da baƙi a jihar bakiɗaya. Yawancin kayan aikinsa sun lalace, wanda hakan ke nuna buƙatar kulawar gaggawa. Bugu da ƙari, asibitin ba shi da isassun kayan aikin ɗakin gwaje-gwaje, wanda ke kawo cikas ga ma’aikatan wajen aiwatar da muhimman hanyoyin gano cututtuka yadda ya kamata.

asibiti

“Manufarmu ba wai don kare lafiya da jin daɗin mazauna jihar da ma’aikatan kiwon lafiya ba ne kawai, sai dai har da magancewa da shawo kan cututtukan da ke yaɗuwa da kuma waɗanda ba sa yaɗuwa.

“Muna da niyyar samar da cikakkiyar tsarin kula da lafiya wanda zai ƙunshi nau’ikan ayyuka masu muhimmanci, gami da samar da magunguna masu muhimmanci, matakan rigakafi, sake fasalin manufofin kiwon lafiya, aiwatar da ƙa’idoji kan tsaftar ruwa da ƙa’idojin tsabtar muhalli, kula da yanayin kiwon lafiya, shirye-shiryen rigakafi, kula da lafiyar mata masu juna biyu, inganta tsarin abinci mai gina jiki gami da ƙarfafa tsarin ba da gudummawar kuɗaɗen kula da lafiya.

“Kamar yadda Asibitin ƙwararru na Yariman Bakura ya kasance shi ne kaɗai cibiyar kula da lafiya mallakar jihar, akwai buƙatar ya samar da kulawa ta musamman da suka shafi haɗaɗɗun matakan jiyya, tare da ba da horo ga ƙananan likitoci da samar da yanayi mai kyau ga ƙwararrun kiwon lafiya da ke gudanar da bincike a fannonin kiwon lafiya daban-daban. Ya zama wajibi mu tabbatar da sake fasalin asibitin. Mun yi niyyar mayar da Yariman Bakura asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Zamfara da zarar an fara Kwalejin Kimiyyar Lafiya.

asibiti

“Abubuwan da za a aiwatar da gyaran a kan su za su haɗa da sabbin gine-gine, faɗaɗawa da inganta gine-ginen da ake da su, gyara gine-ginen da ake da su, da kammala rukunin ginin likitoci, da bunƙasa ɗakin gwaje-gwaje. Haɓaka kayayyakin aiki da inganta cikakken tsarin Kula da Bayanan Asibiti.”

asibiti
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

May 21, 2026
Next Post
Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.