ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asibitin Yariman Bakura Ya Fara Amfana Da Dokar Ta-ɓaci A Sashen Kiwon Lafiyar Zamfara

by Leadership Hausa
2 years ago
asibiti

Asibitin Yariman Bakura da ke Gusau ya fara amfana da dokar ta-ɓaci a sashen kiwon lafiya da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ayyana sakamakon ƙaddamar da aikin gyara, ingantawa da kuma samar da kayan aiki a asibitin ƙwararrun ɗaya tilo mallakar gwamnatin jihar.

An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a ranar Alhamis da ta gabata a asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura da ke Gusau, babban birnin jihar.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa ingantawar za ta mayar da asibitin zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

A yayin jawabinsa a wurin taron, Gwamna Lawal ya tabbatar da cewa, gyaran zai inganta tsarin kula da marasa lafiya ta musamman, da ƙara yawan ma’aikatan kiwon lafiya, da kuma inganta tsarin ayyukan, wanda zai haifar da ingantaccen kiwon lafiya.

“Mun zo nan a yau ne domin ƙaddamar da gyare-gyare da kuma samar da kayan aiki na asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura da ke Gusau. Aikin zai kuma ƙunshi samar da kayan aikin jinya ga asibitin. Wannan aiki dai ya biyo bayan ayyana dokar ta-ɓaci ne a fannin kiwon lafiyar jihar, bayan na ilimi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”

2 – 3 Cikin 10 Na Masu Cutar Diphtheria Na Iya Mutuwa A Katsina – NMA

“Wannan babban ƙalubale ne da muka gada a wannan fanni lokacin da muka karɓi ragamar mulkin jihar.

“Asibitin na cikin mawuyacin hali duk da irin rawar da yake takawa wajen samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga mazauna da baƙi a jihar bakiɗaya. Yawancin kayan aikinsa sun lalace, wanda hakan ke nuna buƙatar kulawar gaggawa. Bugu da ƙari, asibitin ba shi da isassun kayan aikin ɗakin gwaje-gwaje, wanda ke kawo cikas ga ma’aikatan wajen aiwatar da muhimman hanyoyin gano cututtuka yadda ya kamata.

asibiti

“Manufarmu ba wai don kare lafiya da jin daɗin mazauna jihar da ma’aikatan kiwon lafiya ba ne kawai, sai dai har da magancewa da shawo kan cututtukan da ke yaɗuwa da kuma waɗanda ba sa yaɗuwa.

“Muna da niyyar samar da cikakkiyar tsarin kula da lafiya wanda zai ƙunshi nau’ikan ayyuka masu muhimmanci, gami da samar da magunguna masu muhimmanci, matakan rigakafi, sake fasalin manufofin kiwon lafiya, aiwatar da ƙa’idoji kan tsaftar ruwa da ƙa’idojin tsabtar muhalli, kula da yanayin kiwon lafiya, shirye-shiryen rigakafi, kula da lafiyar mata masu juna biyu, inganta tsarin abinci mai gina jiki gami da ƙarfafa tsarin ba da gudummawar kuɗaɗen kula da lafiya.

“Kamar yadda Asibitin ƙwararru na Yariman Bakura ya kasance shi ne kaɗai cibiyar kula da lafiya mallakar jihar, akwai buƙatar ya samar da kulawa ta musamman da suka shafi haɗaɗɗun matakan jiyya, tare da ba da horo ga ƙananan likitoci da samar da yanayi mai kyau ga ƙwararrun kiwon lafiya da ke gudanar da bincike a fannonin kiwon lafiya daban-daban. Ya zama wajibi mu tabbatar da sake fasalin asibitin. Mun yi niyyar mayar da Yariman Bakura asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Zamfara da zarar an fara Kwalejin Kimiyyar Lafiya.

asibiti

“Abubuwan da za a aiwatar da gyaran a kan su za su haɗa da sabbin gine-gine, faɗaɗawa da inganta gine-ginen da ake da su, gyara gine-ginen da ake da su, da kammala rukunin ginin likitoci, da bunƙasa ɗakin gwaje-gwaje. Haɓaka kayayyakin aiki da inganta cikakken tsarin Kula da Bayanan Asibiti.”

asibiti
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

MASU ALAKA

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
Manyan Labarai

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”

September 3, 2026
asibiti
Kiwon Lafiya

2 – 3 Cikin 10 Na Masu Cutar Diphtheria Na Iya Mutuwa A Katsina – NMA

August 30, 2026
Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
Kiwon Lafiya

Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?

August 29, 2026
Next Post
Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.