• Leadership Hausa
Sunday, August 7, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Matasa A Guji Bangar Siyasa, ‘Yan Siyasa Ba Za Su Ba Ku Komai Ba Sai Ƙwaya – Matasan Arewa A Kudu

by yahuzajere
2 months ago
in Labarai
0
Matasa A Guji Bangar Siyasa, ‘Yan Siyasa Ba Za Su Ba Ku Komai Ba Sai Ƙwaya – Matasan Arewa A Kudu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasancewar matasa ƙashin bayan al’umma wanda kuma suka fi fuskantar haɗarin amfani da su wajen cimma muradun miyagun ‘yan siyasa, Gamayyar Matasan Arewa a Kudu da ke Legas, ta yi kira da babbar murya ga ɗaukacin matasan Nijeriya da kar su bari ɓata-garin ‘yan siyasa su riƙa amfani da su a matsayin ‘yan bangar siyasa musamman a halin yanzu da aka shiga kakar siyasa.
Gamayyar ta yi kiran ne ta hannun shugabanta, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci a wani ɓangare na yunƙurin da take yi wajen wayar wa da ‘yan ƙasa kai a game da abubuwan da za su kawo musu ci gaba a rayuwarsu.

  • Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga

A cewar gamayyar, “muna sake tunatarwa ga dukkan matasan Nijeriya da su guji yin bangar siyasa domin rayuwarsu tana cikin haɗari, ɓata-garin ‘yan siyasar ƙasarmu ba za su tsinana musu komai ba illa su yi ɗibga musu kayan maye saboda gusar da hankulansu, domin sun san cewa idan matasan suna cikin hayyacinsu ba za su iya saka su miyagun abubuwa ba a ƙoƙarinsu na cimma burinsu na son zuciya.”

Ƙungiyar ta ce irin yadda ake amfani da ƙazaman kuɗaɗe wajen tsayar da ‘yan takara a jam’iyyu manuniya ce kan irin lalacewar da tsarin siyasar ƙasar nan ya yi.

“Kun ga dai yadda ake sayen daliget, wannan shi ne ya nuna wa duniya cewa tsarin zaɓenmu ya gurɓace. ‘Yan siyasar sun mayar da sha’anin takara na ko-a-mutu-ko-a-yi-rai, sannan duk abubuwan da suke faruwa a arewa na kisan jama’a da sace-sacen dukiyoyinsu da cin zarafin iyalai akwai alamun wasu da ke kan mulki a madafun ikon gwamnati suna da hannu a ciki, haka nan wasu masu neman tsayawa takara, shi ya sa wasu ko ana-ha-maza-ha-mata za su ce dole su ci zaɓe domin rufe asirin miyagun ayyukansu.

“Kowa ya san arewa tana da arzikin ma’adanai masu daraja, shi ya sa da ake son sacewa sai aka kitsa mana kashe-kashe da sace-sace, kuma abin takaici ba mu da shugabanni nagari da za hana. Shi ya sa a kullum yankin komawa baya yake yi, muna sake kira ga jami’an tsaro da su guji harka da ‘yan siyasa domin amana ce suka ɗauka ta kare al’umma ba wasu tsirarun miyagun mutane ba kawai kuma za su yi wa Allah bayani saboda tsakani da talakawan arewa na cikin mawuyacin hali.” In ji shugaban gamayyar.

Labarai Masu Nasaba

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Ƙungiyar ta ce abubuwan da ake yi na rashin kishin ƙasa daga shugabanni ya ƙara sabbaba yunwa, matsalar tsaro da sauran ƙuncin rayuwa, ga kuma abin kunya harkar ilimi ta zama wasa da cin zarafin malaman jami’o’i.

“Yara matasa ‘yan label 400 (ajin ƙarshe) an ɓata musu karatunsu, wasu suna lokacin jarabawa aka rufe jami’o’i, ya kamata shuganinmu nagari su sake jajircewa kuma su ji tsoron Allah su ci gaba da faɗa wa juna gaskiya domin akwai ranar hisabi, abun dubawa a nan a yankin Yarabawa irin waɗannan halayen babu su, haka a yankin Inyamurai, duk inda ka bi mu ‘yan arewa ake kashewa, kuma hakan na ta faruwa tun daga kisan kisan gillar da aka yi wa manyan magabatanmu irin su Sardauna da Tafawa ɓalewa, don haka ya kamata wannan ya zama izina ga duk mai kishin ƙasa.” In ji Galadanci.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

Next Post

Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

Related

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki
Labarai

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

15 mins ago
Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas
Labarai

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

2 hours ago
Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi
Labarai

Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

3 hours ago
NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi
Labarai

NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

5 hours ago
Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa
Labarai

Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

5 hours ago
NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
Labarai

CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

7 hours ago
Next Post
Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

LABARAI MASU NASABA

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

August 7, 2022
Peter Obi Ba Zaiyi Nasarar Lashe Koda Rabin Jihar Nasarawa Ba – Inji Deji Adeyanju

Peter Obi Ba Zaiyi Nasarar Lashe Koda Rabin Jihar Nasarawa Ba – Inji Deji Adeyanju

August 7, 2022
Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

August 7, 2022
MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

August 7, 2022
Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

August 7, 2022
Wakilin Sin Ya Ki Amincewa Da Zargin Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Makamashin Nukiliyar Kasar Sin

Wakilin Sin Ya Ki Amincewa Da Zargin Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Makamashin Nukiliyar Kasar Sin

August 7, 2022
NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

August 7, 2022
Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

August 7, 2022
Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

August 7, 2022
Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Bunkasa Da Kaso 10.4 Bisa Dari Cikin Watanni 7 Na Bana

Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Bunkasa Da Kaso 10.4 Bisa Dari Cikin Watanni 7 Na Bana

August 7, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.