• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasan Arewa maso Gabas Sun Ƙalubalanci Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Ayyukan Gwamnan Kano

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna yusuf
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matasa a ƙarƙashin Ƙungiyar ‘North East Youth Progressive Union’ and Coalition for Democratic Rights Group’, sun ƙalubalanci Gwamnonin Arewa su yi koyi da irin ayyukan inganta rayuwar al’umma, wanda Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ke aiwatarwa.

Matasan sun yi wannan kira a ranar Laraba, a Yola, babban birnin Jihar Adanawa, inda suka yi taron manema labarai.

  • Kwankwaso Ya Kaddamar Da Cibiyar Nazarin Harkokin Alkur’ani
  • Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

Idan za a tuna, Gwamnatin Jihar Kano a ƙarƙashin Gwamna Yusuf ta sake farfaɗo da inganta ilmin ‘ya’yan talakawa, wanda tsohon Gwamna Sanata Rabi’u Kwankwaso ya ƙirƙiro a zamanin mulkin sa.

Shiri ne wanda ke bai wa ‘ya’yan talakawa damammakin samun guraben tafiya karatu kyauta a jami’o’in ƙasar nan da na ƙasashen waje.

Kwanan nan Gwamnatin Kano ta ɗauki nauyin ɗalibai 1001 waɗanda suka tafi ƙaro karatu a Indiya da Uganda kyauta.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Da ya ke jawabi wurin taron, Shugaban Ƙungiyar Dakta Kabir Hassan Sambo, ya nuna damuwar sa dangane da bambancin ratar samun damar ilmi tsakanin Arewa da Kudancin ƙasar nan.

Daga nan, Sambo sai ya bayar da shawarar cewa gwamnonin Arewa su gaggauta ɗaukar salo da tsarin da Gwamnatin Kano ke kai na inganta fannin ilmi, a wannan yanayi da ake fuskantar ƙalubalen rayuwar zamantakewa da ta tattalin arziki.

Sambo ya ce: “Abin dubawa ne sosai ganin yadda Gwamna Yusuf na Jihar Kano a cikin watanni biyar ya biya kuɗaɗen ɗalibai, kuɗin abincin ‘yan makaranta, kuɗin hayar ɗakunan kwanan dalibai 1001 da aka ɗauka suka tafi karatu Indiya.

“Kuma ya biya kuɗin jarabawar NECO ga ɗaliban sakandare 57,000. Sai kuma kuɗin makaranta ga ɗalibai 7,000 a Jami’ar Bayero da wasu manyan makarantu a Kano, waɗanda aka rage wa kashi 50% bisa 100% na kuɗin makarantun jami’o’i.

“Sannan kuma ya samar da cibiyoyin koyon sana’o’i ga matasa har guda 26 a faɗin jihar, domin tallafa masu a Jihar Kano.

“Gaskiya mu na buƙatar dukkan gwamnonin Arewa su yi koyi da tsare-tsaren da Kano ta ke kan yi, wajen bayar da fifiko kan ilmi da bunƙasa rayuwar al’umma.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Kabir YusufIlimi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Daure Mutumin Da Ya Yi Lalata Da Jikar Makocinsa

Next Post

An Kama Dalibin Jami’a Da Ake Zargi Da Kashe Wani Yaro

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

10 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

10 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

12 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

14 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

15 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

16 hours ago
Next Post
An Kama Dalibin Jami’a Da Ake Zargi Da Kashe Wani Yaro

An Kama Dalibin Jami’a Da Ake Zargi Da Kashe Wani Yaro

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.