ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasan Arewa maso Gabas Sun Ƙalubalanci Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Ayyukan Gwamnan Kano

by Sulaiman
3 years ago
Gwamna yusuf

Matasa a ƙarƙashin Ƙungiyar ‘North East Youth Progressive Union’ and Coalition for Democratic Rights Group’, sun ƙalubalanci Gwamnonin Arewa su yi koyi da irin ayyukan inganta rayuwar al’umma, wanda Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ke aiwatarwa.

Matasan sun yi wannan kira a ranar Laraba, a Yola, babban birnin Jihar Adanawa, inda suka yi taron manema labarai.

  • Kwankwaso Ya Kaddamar Da Cibiyar Nazarin Harkokin Alkur’ani
  • Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

Idan za a tuna, Gwamnatin Jihar Kano a ƙarƙashin Gwamna Yusuf ta sake farfaɗo da inganta ilmin ‘ya’yan talakawa, wanda tsohon Gwamna Sanata Rabi’u Kwankwaso ya ƙirƙiro a zamanin mulkin sa.

ADVERTISEMENT

Shiri ne wanda ke bai wa ‘ya’yan talakawa damammakin samun guraben tafiya karatu kyauta a jami’o’in ƙasar nan da na ƙasashen waje.

Kwanan nan Gwamnatin Kano ta ɗauki nauyin ɗalibai 1001 waɗanda suka tafi ƙaro karatu a Indiya da Uganda kyauta.

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

Da ya ke jawabi wurin taron, Shugaban Ƙungiyar Dakta Kabir Hassan Sambo, ya nuna damuwar sa dangane da bambancin ratar samun damar ilmi tsakanin Arewa da Kudancin ƙasar nan.

Daga nan, Sambo sai ya bayar da shawarar cewa gwamnonin Arewa su gaggauta ɗaukar salo da tsarin da Gwamnatin Kano ke kai na inganta fannin ilmi, a wannan yanayi da ake fuskantar ƙalubalen rayuwar zamantakewa da ta tattalin arziki.

Sambo ya ce: “Abin dubawa ne sosai ganin yadda Gwamna Yusuf na Jihar Kano a cikin watanni biyar ya biya kuɗaɗen ɗalibai, kuɗin abincin ‘yan makaranta, kuɗin hayar ɗakunan kwanan dalibai 1001 da aka ɗauka suka tafi karatu Indiya.

“Kuma ya biya kuɗin jarabawar NECO ga ɗaliban sakandare 57,000. Sai kuma kuɗin makaranta ga ɗalibai 7,000 a Jami’ar Bayero da wasu manyan makarantu a Kano, waɗanda aka rage wa kashi 50% bisa 100% na kuɗin makarantun jami’o’i.

“Sannan kuma ya samar da cibiyoyin koyon sana’o’i ga matasa har guda 26 a faɗin jihar, domin tallafa masu a Jihar Kano.

“Gaskiya mu na buƙatar dukkan gwamnonin Arewa su yi koyi da tsare-tsaren da Kano ta ke kan yi, wajen bayar da fifiko kan ilmi da bunƙasa rayuwar al’umma.”

Kano
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana
  • Sulaiman
    Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD
  • Sulaiman
    Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani
  • Sulaiman
    Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

MASU ALAKA

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir
Labarai

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

July 20, 2026
Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi
Labarai

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

July 20, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu
Manyan Labarai

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Next Post
An Kama Dalibin Jami’a Da Ake Zargi Da Kashe Wani Yaro

An Kama Dalibin Jami’a Da Ake Zargi Da Kashe Wani Yaro

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

July 20, 2026
Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

July 20, 2026
Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

July 20, 2026
NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

July 20, 2026
Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

July 20, 2026
Sin Ta Zamo Kan Gaba A Duniya A Fannin Kirar Mutum-Mutumin Inji

Sin Ta Zamo Kan Gaba A Duniya A Fannin Kirar Mutum-Mutumin Inji

July 20, 2026
Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

July 20, 2026
Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

July 20, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.