ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasan Arewa maso Gabas Sun Ƙalubalanci Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Ayyukan Gwamnan Kano

by Sulaiman
3 years ago
Gwamna yusuf

Matasa a ƙarƙashin Ƙungiyar ‘North East Youth Progressive Union’ and Coalition for Democratic Rights Group’, sun ƙalubalanci Gwamnonin Arewa su yi koyi da irin ayyukan inganta rayuwar al’umma, wanda Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ke aiwatarwa.

Matasan sun yi wannan kira a ranar Laraba, a Yola, babban birnin Jihar Adanawa, inda suka yi taron manema labarai.

  • Kwankwaso Ya Kaddamar Da Cibiyar Nazarin Harkokin Alkur’ani
  • Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

Idan za a tuna, Gwamnatin Jihar Kano a ƙarƙashin Gwamna Yusuf ta sake farfaɗo da inganta ilmin ‘ya’yan talakawa, wanda tsohon Gwamna Sanata Rabi’u Kwankwaso ya ƙirƙiro a zamanin mulkin sa.

ADVERTISEMENT

Shiri ne wanda ke bai wa ‘ya’yan talakawa damammakin samun guraben tafiya karatu kyauta a jami’o’in ƙasar nan da na ƙasashen waje.

Kwanan nan Gwamnatin Kano ta ɗauki nauyin ɗalibai 1001 waɗanda suka tafi ƙaro karatu a Indiya da Uganda kyauta.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

Da ya ke jawabi wurin taron, Shugaban Ƙungiyar Dakta Kabir Hassan Sambo, ya nuna damuwar sa dangane da bambancin ratar samun damar ilmi tsakanin Arewa da Kudancin ƙasar nan.

Daga nan, Sambo sai ya bayar da shawarar cewa gwamnonin Arewa su gaggauta ɗaukar salo da tsarin da Gwamnatin Kano ke kai na inganta fannin ilmi, a wannan yanayi da ake fuskantar ƙalubalen rayuwar zamantakewa da ta tattalin arziki.

Sambo ya ce: “Abin dubawa ne sosai ganin yadda Gwamna Yusuf na Jihar Kano a cikin watanni biyar ya biya kuɗaɗen ɗalibai, kuɗin abincin ‘yan makaranta, kuɗin hayar ɗakunan kwanan dalibai 1001 da aka ɗauka suka tafi karatu Indiya.

“Kuma ya biya kuɗin jarabawar NECO ga ɗaliban sakandare 57,000. Sai kuma kuɗin makaranta ga ɗalibai 7,000 a Jami’ar Bayero da wasu manyan makarantu a Kano, waɗanda aka rage wa kashi 50% bisa 100% na kuɗin makarantun jami’o’i.

“Sannan kuma ya samar da cibiyoyin koyon sana’o’i ga matasa har guda 26 a faɗin jihar, domin tallafa masu a Jihar Kano.

“Gaskiya mu na buƙatar dukkan gwamnonin Arewa su yi koyi da tsare-tsaren da Kano ta ke kan yi, wajen bayar da fifiko kan ilmi da bunƙasa rayuwar al’umma.”

Kano
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato
Labarai

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Manyan Labarai

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Next Post
An Kama Dalibin Jami’a Da Ake Zargi Da Kashe Wani Yaro

An Kama Dalibin Jami’a Da Ake Zargi Da Kashe Wani Yaro

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.