• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

bySani Anwar
1 week ago
Baya

Matsalar tasgadewar kashin baya, na faruwa musamman da kananan yara masu tasowa daga tsakanin shekara tara zuwa sha hudu, yayin da kasusuwansu suka fi jan gaba.

Wadanda ke gamuwa da wannan matsala, sun kai kamar kashi uku cikin 100 na kananan yara masu tasowa. Haka nan, matsalar ta fi faruwa ga ‘ya’ya mata, duk da cewa; wannan matsala na iya shafar kowa, sannan kuma a kowane irin shekaru.

  • Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI
  • A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

Haka zalika, wannan matsala na faruwa ne a yayin da wasu daga cikin jerin kasusuwan baya suka yi baka ko suka karkace zuwa hagu ko dama tare da murdewar jerin kasusuwan bayan.

Wannan baka ko karkacewa, na iya faruwa a ko’ina a jerin kasusuwan baya daga sama zuwa kasa. Wani yana yin sifar baka ko harafin ‘C’, ko kuma harafin ‘S’.

Sai dai, kashi 70 zuwa 80 cikin 100 na wannan matsala, ba a san hakikanin dalilan faruwarta ba. Sai dai, matsalar ta fi yin kamari ga yara masu lalurar shan-inna, yaran da aka haifa da shanyewar kwakwalwa ko wadanda aka haifa da tawayar kashin gadon baya.

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

An raba nakasun bakan baya ko tasgadewar kashin bayan zuwa mataki uku a ma’aunin kusurwa na “Cobb angle”:

Mataki na farko: Mafi karancin nakasu (Cobb 10-25°)

Mataki na biyu: Matsakaicin nakasu (Cobb 26-40°)

Mataki na uku: Matsanancin nakasu (Cobb 50° zuwa sama).

A Mataki na daya da na biyu, likitan fisiyo na taimakawa wajen shawo kan matsalar da kuma magance ci gaban matsalar zuwa mataki na uku (Matsanancin nakasu), wanda sai ya bukaci yin aiki ko tiyata, domin gyara tasgadewar kashin bayan.

Matsalolin da ke tattare da tasgadewar kashin baya sun hada da:

1- Tawayar surar jiki

2- Matsalolin numfashi

3- Raguwar ingancin rayuwa da sauran makamantansu.

Haka nan kuma, matsalar na faruwa kadan da kadan ba tare da jin wani ciwo ba, sai dai; ana iya gamuwa da ciwon baya, ciwon kafada idan matsalar ta ta’azzara.

Ta yaya za a gane yaro ko yarinya na da wannan matsala?

Hanya mafi sauki da iyaye za su gane idan ‘ya’yansu suna da matsalar ta hada da sanya ido a gadon bayansu yayin sanya tufafi.

Abubuwan lura sun hada da cewa:

1- Kowace kafada ta yi saiti daidai ba tare da wata ta fi wata tudu ba.

2- Kowane allon kafada yana danfare da uwar jiki ba tare da daya ya bullo baya fiye da dayan ba.

3- Tsayin hannaye ya zamo bai-daya a yayin tsaiwa, ba tare da dya ya fi daya sauka kasa ba.

4- Gadon baya ya zamo bai-daya a yayin da aka durkusa (kamar yin ruku’u, amma tare da sakin hannaye zuwa kasa), ba tare da ganin wani doro a bangare daya na gadon baya ba, musamman a bangaren hakarkarin baya ko kasan allon kafada daya.

5- Gadon baya, ya zamo a mike yayin tsaiwa; ba tare da bayyanar siffar baka ko tasgadewa a tsakiyar gadon bayan ba.

Da zarar an lura da matsalar bakan baya, sai a yi maza a tuntubi likitan, domin magance matsalar tun da wuri kafin ta ta’azzara; har ta tilasta yin tiyatar baya, domin rike kasusuwan gadon baya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?
Kiwon Lafiya

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi
Kiwon Lafiya

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Next Post
Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version