• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Gwamnan Zamfara Ya Nanata Bukatar Amfani Da Fasahar Zamani

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada bukatar amfani da manyan na’urorin zamani domin yaki da matsalar tsaro a Jihar Zamfara, Arewa da ma Nijeriya baki daya.
Gwamnan Jihar Zamfara da wasu gwamnonin jihohi sun gana da Amina J. Mohammed, Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya a birnin Washington D.C. ranar Juma’a.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar ta bayyana cewa taron ya samu halartar gwamnonin jihohin Zamfara, Benuwai, Jigawa, Kaduna, Katsina, Kebbi, da Neja.
Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Amina J. Mohammed ta yaba wa Gwamnonin kan kokarin da suke yi na ganin an magance matsalolin yankin.
“Kasancewar ku a nan ya nuna kwakkwarar sha’awar da Gwamnonin Arewa ke yi na aiwatar da sauyi a jihohinsu.

  • Yadda Sojoji Suka Fatattaki ‘Yan Bindiga Tare Da Ceto Mutane 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Dokar Amurka Ta Ba Da Tallafin Kudi Ga Wasu Kasashe Ta Hargitsa Duniya

Da yake bayyana halin da ake ciki a Zamfara ga Mataimakiyar Babban Sakataren, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana muhimmiyar rawar da fasahar zamani za ta iya takawa wajen inganta tsaro da kuma bukatar hada karfi da karfe wajen amfani da karfin fasahar da ta hada da yin amfani da fasahar kere-kere, na’urorin tantance kwayoyin halitta da kyamarorin sa ido (CCTV).

“Muna nan da matsalolin da dama, amma babban kalubalenmu shi ne rashin tsaro, kuma dole ne a yi wani abu a kai.
“Saboda rashin tsaro, noma ya gagara. Muna bukatar taimako wajen bunkasa noma ta yadda za mu iya amfani fasaha wajen yaki da wannan tada kayar baya. Muna fatan samun mafita ga wadannan matsalolin yayin wadannan tarukan. Na karbi mulki a jiha mai cike da rashin aiki tare da karancin ci gaba.

“Na ayyana dokar ta-baci a fannin ilimi da lafiya. Dole ne mu dauki matakin gaggawa don magance wadannan batutuwa masu muhimmanci; in ba haka ba, makomar mu za ta yi muni. Muna bukatar tallafi mai muhimmanci don shawo kan wadannan kalubalen da kuma tabbatar da kyakkyawar makoma ga jama’armu.”

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Tinubu Zai Hakura Da Ganduje Ya Rungumi Kwankwaso?

Next Post

Sarkin Kano Ya Shawarci Ministan Sadarwa Kan Amfani Da Fasaha

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

1 month ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

3 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

3 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

3 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

8 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

8 months ago
Next Post
Sarkin Kano Ya Shawarci Ministan Sadarwa Kan Amfani Da Fasaha

Sarkin Kano Ya Shawarci Ministan Sadarwa Kan Amfani Da Fasaha

LABARAI MASU NASABA

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

May 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

May 30, 2025
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

May 30, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 30-03-2025

May 30, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano

An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.