ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

by Khalid Idris Doya and Abubakar Sulaiman
2 years ago
Mantuwa

Masana lafiyar kwakwalwa sun ce yawan mantuwa na taka rawa wajen samun zuciya mai sauki, kamar yadda Charan Ranganath wani masanin lafiyar kwakwalwa ya rubuta a cikin wani sabon littafinsa.

 

Masanin ya ce dalilin da ya sa kwakwalwa ke tuna abin da ya wuce, yana da alaka da yadda mutum ke kallon kansa da kuma sauran mutane da yadda duniya take.

ADVERTISEMENT
  • APP Ta Lashe Kujeru 22 A Zaben Kananan Hukumomin Ribas
  • Sin Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaron MDD Da Kada Ya Yi Watsi Da Bincike Game Da Fashewar Bututun Gas Na Nord Stream

Farfesa Ranganath, wanda ya kwashe shekara talatin yana karantar da halayyar Dan’adam da yadda Dan’adam ke tunani tare da hanyoyin tuna abin da ya wuce da mantuwa, ya ce yawancin bayanan da ake bayarwa kan mantuwa ba haka suke ba, saboda mantuwa na bayar da gudummawa cikin rayuwar muyane.

 

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Masanin lafiyar kwakwalwar ya tattauna da Dabid Robson, dan jarida a fannin kimiyya, kan yadda mutane za su fahimci kwakwalwarsu domin samun kwanciyar hankali.

 

Dan’adam na iya ajiye abu a kwakwalwarsa da taimakon sauye-sauyen da ake samu na alakar da ke tsakanin kwayoyin da ke isar da sako, ka’idar koyo bisa kuskure ita ce, lokacin da kuke kokarin tuno abubuwan da suka wuce, kwakwalwa na fitar da abubuwa masu kyau tare da kokarin tauye wadanda ba su da kyau ta hanyar alakanta bayanan da na gaskiya.

 

Wannan yana nufin cewa hanya mafi kyau don karin koyo ita ce mutum ya kalubalanci kansa domin nemo abubuwan da muke son koyo, saboda ta haka ne mutum zai gane inda kwakwalwarsa ke da rauni, kuma hakan zai kara taimaka wa kwakwalwa wajen tuna abubuwan da suka faru.

 

Shi ya sa a ko da yaushe ana son mutum ya rika kokarin sanin wani abu, kamar misali, idan za ka je wani wuri da ba ka sani ba, maimakon ka yi amfani da manhajar Google, sai mutum ya yi amfani da kwakwalwarsa ko ta hanyar tambaya domin gano wurin, hakan na da matukar tasiri.

 

“Matsalar ita ce, yayin da muke girma, shekaru na kama mu, ba lalle ba ne a ce ba ma iya haddace abubuwa, illa dai a ce ba ma mayar da hankali a kan bayanan da ya kamata mu tuna.

 

“Abubuwa na dauke mana hankali, kuma dukkanin wadannan abubuwa da ba su da muhimmanci, suna dauke mana hankali maimakon mu bayar da muhimmanci ga abubuwan da ke da amfani garemu.

 

“Saboda haka idan muka bukaci tuna wadannan abubuwa, sai mu kasa samun bayanin da muke nema.

 

“Masanin ya ba da shawarori na yadda za su taimama. Ta farko, ita ce abu ya kasance fitacce na daban. Abubuwan da muke sanya wa kwakwalwarmu suna gogayya ne da juna, saboda haka duk abin da ka fi yawan amfani ko ambato zai fi zama a kwakwalwarka.

 

“Bayanan da ke kwakwalwarmu masu alaka da wasu hotuna na daban ko na musamman da sauti da ji a jika, su ne wadanda suke zama a kwakwalwarmu.

 

“Mayar da hankali kan bayanai masu muhimmanci da jikinmu ya ji ko ya san su, maimakon haddace su, ya fi taimaka mana haddace abubuwa.

 

“Dabara ta biyu ita ce, mutum ya mayar da hankali wajen tsara abubuwa a kwakwalwarsa, domin ya ba su ma’ana sosai. A littafin, ya tattauna kan tsarin gurbin hadda, wanda ya kunshi danganta bayanin da kake son ka koya da bayanin da kake da shi daman a kwakwalwarka.

Mantuwa
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Mantuwa
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Asalin Tushen Matsalolinmu A Nijeriya

Asalin Tushen Matsalolinmu A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.