ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Tinubu Zai Hakura Da Ganduje Ya Rungumi Kwankwaso?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Dambarwar sanar da dakatar da Abdullahi Umar Ganduje daga Jam’iyyar APC a mazabarsa da ke Dawakin Tofa a Jihar Kano da sake sanar soke dakatarwar da babbar kotun Jihar Kano ta yi a farkon makon nan bayan da farko ta ce ta tabbatar, na ci gaba da janyo ce-ce-ku-ce inda har ma wasu sun fara tunanin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, da yiwuwar ya hakura da Ganduje ya kama Rabiu Musa Kwankwaso a Jihar Kano.

Dama dai magoya bayan Ganduje ba su ji dadi ba lokacin da Kwankwaso ya gana da Tinubu a Birnin Paris na kasar Faransa kafin a rantsar da shi da kuma ganawar da suka yi a watan Yuni a fadar shugaban kasa bayan ya shiga ofis.

  • Hajji: Saudiyya Ta Gargadi Kamfanonin Bogi Kan Aikata Damfara, Ta Jadadda Muhimmancin Biza Ga Mahajjata
  • Duk Da Matsin Rayuwa: Hukumomi 7 Sun Kebe Wa Kansu Naira Biliyan 80.9 Na Jin Dadi

A karshin ganawar na watan Yuni, dan takarar jam’iyyar NNPP a zaben 2023 ya bayyana wa ‘yan jarida ceewa sun tattauna harkokin siyasa da kuma na shugabanci shi da Shugaban Tinubu. Har zuwa yau mataimaka Tinubu da na Kwankwaso ba su bayyana cikakken bayani kan wannan tattaunawar ba. Da wannan ne wasu suke gabin akwai lauje cikin nadi.

ADVERTISEMENT

Daga adadin masu jefa kuri’a da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta fitar a zaben 2023 mutum 93, 469,008, Jihar Legas ce ta fi kowacce yawa da mutum 7,060,195, sai kuma Jihar Kano da ke mara mata baya da mutum 5,921,370. Wannan ya sa jihohin biyu suke da matukar muhimmanci ga kowane dan Takara.

Nasarar da jam’iyyar NNPP ta yi a kotun koli ta kara yin tasiri a bangaren siyasa kan abokiyar hamayyarta ta APC wanda Ganduje yake shugabanta.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

A ra’ayin wasu, kamar yadda kuma wadanda suka ce sun dakatar da Ganduje daga APC suka ba da hujja a kai kan zargin cin hanci da rashawa, Tinubu zai iya fakewa da hakan ya ajiye Ganduje a gefe ya rungumi Kwankwaso. Wasu ma na ganin cewa da gangan aka tayar da wannan bincike domin a kawar da Ganduje a janyo Kwankwaso.

Bisa burin shugaban kasa na ci gaba da samun nasara a zaben 2027, dole yana bukatar mutanen da za su iya sama masa kuri’u masu yawa kamar irinsu Kwankwaso wanda ake ganin yana da tasirin siyasa a Jihar Kano.

Duk da haka, akwai jigon jam’iyyar APC wanda ya yi watsi da cewa Tinubu zai hakura da Ganduje ya rungumi Kwankwaso.

Ya ce, “Tinubu dan siyasa ne mai mayar da alkairi ga duk wanda ya yi masa wahala. Ba zai taba yarda ya watsar da mutane kamar irinsu Ganduje ba. Ya san cewa har yanzu Kwankwaso bai karaya ba da burinsa na zama shugaban kasa ba. Yana da matukar hatsari ya bari jam’iyyar APC ta tarwatse a hannunsa, saboda yana kadayin janyo dan siyasa kamar Kwankwaso ya shigo APC.”
Da yake tarbar shugabannin APC na Jihar Kano a sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja, Ganduje ya zargi gwamnatin Kano da shafa masa kashin kaji a matsayinsa na shugaban APC domin rage wa Tinubu karfi a yankin arewa maso yamma a zaben 2027.

Ya yi ikirarin cewa wannan siyasa ce domin kawar da hankalin mutane daga gazawar gwamnatin NNPP da ke jagorantar Jihar Kano. Ya ce lallai shugaban kasa ya tabbatar masa da cewa shi ne ya sani a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

A wannan gaba, wasu na ganin Ganduje yana da goyon bayan shugaban kasa ba zai taba yuwuwa ba a watsar da shi a kama Kwankwaso, yayin da wasu suke ganin an kisa wannan bincike ne domin tunbuke Ganduje daga shugabancin jam’iyya tare da janyo Kwankwaso a jiki.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Lawal

Matsalar Tsaro: Gwamnan Zamfara Ya Nanata Bukatar Amfani Da Fasahar Zamani

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.