ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Tinubu Zai Hakura Da Ganduje Ya Rungumi Kwankwaso?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Dambarwar sanar da dakatar da Abdullahi Umar Ganduje daga Jam’iyyar APC a mazabarsa da ke Dawakin Tofa a Jihar Kano da sake sanar soke dakatarwar da babbar kotun Jihar Kano ta yi a farkon makon nan bayan da farko ta ce ta tabbatar, na ci gaba da janyo ce-ce-ku-ce inda har ma wasu sun fara tunanin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, da yiwuwar ya hakura da Ganduje ya kama Rabiu Musa Kwankwaso a Jihar Kano.

Dama dai magoya bayan Ganduje ba su ji dadi ba lokacin da Kwankwaso ya gana da Tinubu a Birnin Paris na kasar Faransa kafin a rantsar da shi da kuma ganawar da suka yi a watan Yuni a fadar shugaban kasa bayan ya shiga ofis.

  • Hajji: Saudiyya Ta Gargadi Kamfanonin Bogi Kan Aikata Damfara, Ta Jadadda Muhimmancin Biza Ga Mahajjata
  • Duk Da Matsin Rayuwa: Hukumomi 7 Sun Kebe Wa Kansu Naira Biliyan 80.9 Na Jin Dadi

A karshin ganawar na watan Yuni, dan takarar jam’iyyar NNPP a zaben 2023 ya bayyana wa ‘yan jarida ceewa sun tattauna harkokin siyasa da kuma na shugabanci shi da Shugaban Tinubu. Har zuwa yau mataimaka Tinubu da na Kwankwaso ba su bayyana cikakken bayani kan wannan tattaunawar ba. Da wannan ne wasu suke gabin akwai lauje cikin nadi.

ADVERTISEMENT

Daga adadin masu jefa kuri’a da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta fitar a zaben 2023 mutum 93, 469,008, Jihar Legas ce ta fi kowacce yawa da mutum 7,060,195, sai kuma Jihar Kano da ke mara mata baya da mutum 5,921,370. Wannan ya sa jihohin biyu suke da matukar muhimmanci ga kowane dan Takara.

Nasarar da jam’iyyar NNPP ta yi a kotun koli ta kara yin tasiri a bangaren siyasa kan abokiyar hamayyarta ta APC wanda Ganduje yake shugabanta.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

A ra’ayin wasu, kamar yadda kuma wadanda suka ce sun dakatar da Ganduje daga APC suka ba da hujja a kai kan zargin cin hanci da rashawa, Tinubu zai iya fakewa da hakan ya ajiye Ganduje a gefe ya rungumi Kwankwaso. Wasu ma na ganin cewa da gangan aka tayar da wannan bincike domin a kawar da Ganduje a janyo Kwankwaso.

Bisa burin shugaban kasa na ci gaba da samun nasara a zaben 2027, dole yana bukatar mutanen da za su iya sama masa kuri’u masu yawa kamar irinsu Kwankwaso wanda ake ganin yana da tasirin siyasa a Jihar Kano.

Duk da haka, akwai jigon jam’iyyar APC wanda ya yi watsi da cewa Tinubu zai hakura da Ganduje ya rungumi Kwankwaso.

Ya ce, “Tinubu dan siyasa ne mai mayar da alkairi ga duk wanda ya yi masa wahala. Ba zai taba yarda ya watsar da mutane kamar irinsu Ganduje ba. Ya san cewa har yanzu Kwankwaso bai karaya ba da burinsa na zama shugaban kasa ba. Yana da matukar hatsari ya bari jam’iyyar APC ta tarwatse a hannunsa, saboda yana kadayin janyo dan siyasa kamar Kwankwaso ya shigo APC.”
Da yake tarbar shugabannin APC na Jihar Kano a sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja, Ganduje ya zargi gwamnatin Kano da shafa masa kashin kaji a matsayinsa na shugaban APC domin rage wa Tinubu karfi a yankin arewa maso yamma a zaben 2027.

Ya yi ikirarin cewa wannan siyasa ce domin kawar da hankalin mutane daga gazawar gwamnatin NNPP da ke jagorantar Jihar Kano. Ya ce lallai shugaban kasa ya tabbatar masa da cewa shi ne ya sani a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

A wannan gaba, wasu na ganin Ganduje yana da goyon bayan shugaban kasa ba zai taba yuwuwa ba a watsar da shi a kama Kwankwaso, yayin da wasu suke ganin an kisa wannan bincike ne domin tunbuke Ganduje daga shugabancin jam’iyya tare da janyo Kwankwaso a jiki.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Lawal

Matsalar Tsaro: Gwamnan Zamfara Ya Nanata Bukatar Amfani Da Fasahar Zamani

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.