ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Tinubu Zai Hakura Da Ganduje Ya Rungumi Kwankwaso?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Dambarwar sanar da dakatar da Abdullahi Umar Ganduje daga Jam’iyyar APC a mazabarsa da ke Dawakin Tofa a Jihar Kano da sake sanar soke dakatarwar da babbar kotun Jihar Kano ta yi a farkon makon nan bayan da farko ta ce ta tabbatar, na ci gaba da janyo ce-ce-ku-ce inda har ma wasu sun fara tunanin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, da yiwuwar ya hakura da Ganduje ya kama Rabiu Musa Kwankwaso a Jihar Kano.

Dama dai magoya bayan Ganduje ba su ji dadi ba lokacin da Kwankwaso ya gana da Tinubu a Birnin Paris na kasar Faransa kafin a rantsar da shi da kuma ganawar da suka yi a watan Yuni a fadar shugaban kasa bayan ya shiga ofis.

  • Hajji: Saudiyya Ta Gargadi Kamfanonin Bogi Kan Aikata Damfara, Ta Jadadda Muhimmancin Biza Ga Mahajjata
  • Duk Da Matsin Rayuwa: Hukumomi 7 Sun Kebe Wa Kansu Naira Biliyan 80.9 Na Jin Dadi

A karshin ganawar na watan Yuni, dan takarar jam’iyyar NNPP a zaben 2023 ya bayyana wa ‘yan jarida ceewa sun tattauna harkokin siyasa da kuma na shugabanci shi da Shugaban Tinubu. Har zuwa yau mataimaka Tinubu da na Kwankwaso ba su bayyana cikakken bayani kan wannan tattaunawar ba. Da wannan ne wasu suke gabin akwai lauje cikin nadi.

ADVERTISEMENT

Daga adadin masu jefa kuri’a da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta fitar a zaben 2023 mutum 93, 469,008, Jihar Legas ce ta fi kowacce yawa da mutum 7,060,195, sai kuma Jihar Kano da ke mara mata baya da mutum 5,921,370. Wannan ya sa jihohin biyu suke da matukar muhimmanci ga kowane dan Takara.

Nasarar da jam’iyyar NNPP ta yi a kotun koli ta kara yin tasiri a bangaren siyasa kan abokiyar hamayyarta ta APC wanda Ganduje yake shugabanta.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

A ra’ayin wasu, kamar yadda kuma wadanda suka ce sun dakatar da Ganduje daga APC suka ba da hujja a kai kan zargin cin hanci da rashawa, Tinubu zai iya fakewa da hakan ya ajiye Ganduje a gefe ya rungumi Kwankwaso. Wasu ma na ganin cewa da gangan aka tayar da wannan bincike domin a kawar da Ganduje a janyo Kwankwaso.

Bisa burin shugaban kasa na ci gaba da samun nasara a zaben 2027, dole yana bukatar mutanen da za su iya sama masa kuri’u masu yawa kamar irinsu Kwankwaso wanda ake ganin yana da tasirin siyasa a Jihar Kano.

Duk da haka, akwai jigon jam’iyyar APC wanda ya yi watsi da cewa Tinubu zai hakura da Ganduje ya rungumi Kwankwaso.

Ya ce, “Tinubu dan siyasa ne mai mayar da alkairi ga duk wanda ya yi masa wahala. Ba zai taba yarda ya watsar da mutane kamar irinsu Ganduje ba. Ya san cewa har yanzu Kwankwaso bai karaya ba da burinsa na zama shugaban kasa ba. Yana da matukar hatsari ya bari jam’iyyar APC ta tarwatse a hannunsa, saboda yana kadayin janyo dan siyasa kamar Kwankwaso ya shigo APC.”
Da yake tarbar shugabannin APC na Jihar Kano a sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja, Ganduje ya zargi gwamnatin Kano da shafa masa kashin kaji a matsayinsa na shugaban APC domin rage wa Tinubu karfi a yankin arewa maso yamma a zaben 2027.

Ya yi ikirarin cewa wannan siyasa ce domin kawar da hankalin mutane daga gazawar gwamnatin NNPP da ke jagorantar Jihar Kano. Ya ce lallai shugaban kasa ya tabbatar masa da cewa shi ne ya sani a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

A wannan gaba, wasu na ganin Ganduje yana da goyon bayan shugaban kasa ba zai taba yuwuwa ba a watsar da shi a kama Kwankwaso, yayin da wasu suke ganin an kisa wannan bincike ne domin tunbuke Ganduje daga shugabancin jam’iyya tare da janyo Kwankwaso a jiki.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Lawal

Matsalar Tsaro: Gwamnan Zamfara Ya Nanata Bukatar Amfani Da Fasahar Zamani

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.