• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Zamfara Da Katsina Sun Gana Da Ministan Tsaro Da Ribaɗu

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Matsalar Tsaro: Gwamnonin Zamfara Da Katsina Sun Gana Da Ministan Tsaro Da Ribaɗu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal da takwaransa na jihar Katsina Dikko Umar Raɗɗa sun yi wata ganawar sirri da Ministan tsar, Badaru Abubakar da mai bai wa shugaba ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribaɗu.

 

Waɗannan ganawa guda biyu sun gudana ne a jiya Talata a ma’aikatar tsaro ta tarayya da kuma ofishin mai bai wa shugaban ƙasan shawara kan harkokin tsaro.

  • Za Mu Fara Kamen Mabarata A Abuja – Wike
  • An Watsa Shirin Bidiyo Zagaye Na 3 Mai Taken “Bayanan Magabata Da Xi Jinping Yake So” A Rasha

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau, ya bayyana cewa, taron ya yi zuzzurfan tattaunawa game da shawarwarin da haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙungiyoyin Arewa ta ‘Coalition of Northern Groups (CNG)’ ta bayar.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Sanarwar ta yi ƙarin haske da cewa, haɗaɗɗiyar ƙungiyar ‘yan Arewar ta gudanar da wani taro ne na kwana biyu a Abuja a ranar 23 ga watan Janairun 2024, wanda tsohon shugaban ƙasa, Janar Abdussalami Abubakar ya shugabanta.

 

Sanarwar ta Idris ta ce, “jiya Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara da Gwamna Dikko Umar Raɗɗa na jihar Katsina sun gana da Ministan tsaro Badaru Abubakar a ma’aikatar tsaro da ke Abuja.

 

“Gwamnonin sun tattauna muhimman batutuwan da suka shafi tsaro a jihohin biyu, tare da samar da hanyoyin bi, bisa haɗin gwiwa da ma’aikatar tsaron don magance matsalar.

 

“Bayan zaman da ya gudana ma’aikatar rsaron, sai Gwamnonin biyu tare da Ministan tsaron, suka wuce zuwa ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro don gudanar da wani zaman na musamman.

 

“A wannan zaman tattaunawar ne suka amince da shawarwarin da aka bayar da wancan taro, wanda haɗaɗɗiyar ƙungiyar ‘yan Arewar ta bayar.

 

“A cikin watan Janairun shekarar nan ne haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙungiyoyin Arewa ta gabatar da wani taron tattaunawa, wanda tsohon shugaban ƙasa, Janar Abdussalami Abubakar, tare da halartar wasu fitattun masu ruwa da tsaki daga yankin Arewacin ƙasar nan.

 

“Aiwatar da waɗannan shawawarin da wannan kwamiti na tsaro ya bayar, zai taimaka matuƙa wajen magance wannan tsalar tsaro mai rikitarwa da ta addabi Arewa Nijeriya.

 

“Wannan na cikin dabarbaru da haɗin gwiwar da waɗannan gwamnoni na Zamfara da Katsina suke bi don ganin sun kawo ƙarshen ‘yan bindiga a jihohin su.

 

Wakilan wannan Ƙungiya ta ‘Coalition of Northern Groups (CNG)’ na cikin wannan tattaunawa da aka yi, bisa wakilcin shugaban kwamitin amintattu na Ƙungiyar, Nastura Ashiru Shariff; shugaban kwamitin tsaro na ƙungiyar, Alhaji Bashir Yusuf; Alhaji Ibrahim Ahmed Katsina; Janar Sarkin Yaki Bello, Ambasada Buhari Bala da Janar Sa’ad Abubakar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Matsalar TsaroTa'addanci 'yan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Taron Tattaunawar Kafofin Watsa Labarai Na Kazan Na Kasashen BRICS

Next Post

Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano

Related

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

7 hours ago
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
Labarai

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

9 hours ago
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

9 hours ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

9 hours ago
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
Labarai

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

10 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

10 hours ago
Next Post
Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano

Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.