ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Zamfara Da Katsina Sun Gana Da Ministan Tsaro Da Ribaɗu

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal da takwaransa na jihar Katsina Dikko Umar Raɗɗa sun yi wata ganawar sirri da Ministan tsar, Badaru Abubakar da mai bai wa shugaba ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribaɗu.

 

Waɗannan ganawa guda biyu sun gudana ne a jiya Talata a ma’aikatar tsaro ta tarayya da kuma ofishin mai bai wa shugaban ƙasan shawara kan harkokin tsaro.

ADVERTISEMENT
  • Za Mu Fara Kamen Mabarata A Abuja – Wike
  • An Watsa Shirin Bidiyo Zagaye Na 3 Mai Taken “Bayanan Magabata Da Xi Jinping Yake So” A Rasha

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau, ya bayyana cewa, taron ya yi zuzzurfan tattaunawa game da shawarwarin da haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙungiyoyin Arewa ta ‘Coalition of Northern Groups (CNG)’ ta bayar.

 

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Sanarwar ta yi ƙarin haske da cewa, haɗaɗɗiyar ƙungiyar ‘yan Arewar ta gudanar da wani taro ne na kwana biyu a Abuja a ranar 23 ga watan Janairun 2024, wanda tsohon shugaban ƙasa, Janar Abdussalami Abubakar ya shugabanta.

 

Sanarwar ta Idris ta ce, “jiya Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara da Gwamna Dikko Umar Raɗɗa na jihar Katsina sun gana da Ministan tsaro Badaru Abubakar a ma’aikatar tsaro da ke Abuja.

 

“Gwamnonin sun tattauna muhimman batutuwan da suka shafi tsaro a jihohin biyu, tare da samar da hanyoyin bi, bisa haɗin gwiwa da ma’aikatar tsaron don magance matsalar.

 

“Bayan zaman da ya gudana ma’aikatar rsaron, sai Gwamnonin biyu tare da Ministan tsaron, suka wuce zuwa ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro don gudanar da wani zaman na musamman.

 

“A wannan zaman tattaunawar ne suka amince da shawarwarin da aka bayar da wancan taro, wanda haɗaɗɗiyar ƙungiyar ‘yan Arewar ta bayar.

 

“A cikin watan Janairun shekarar nan ne haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙungiyoyin Arewa ta gabatar da wani taron tattaunawa, wanda tsohon shugaban ƙasa, Janar Abdussalami Abubakar, tare da halartar wasu fitattun masu ruwa da tsaki daga yankin Arewacin ƙasar nan.

 

“Aiwatar da waɗannan shawawarin da wannan kwamiti na tsaro ya bayar, zai taimaka matuƙa wajen magance wannan tsalar tsaro mai rikitarwa da ta addabi Arewa Nijeriya.

 

“Wannan na cikin dabarbaru da haɗin gwiwar da waɗannan gwamnoni na Zamfara da Katsina suke bi don ganin sun kawo ƙarshen ‘yan bindiga a jihohin su.

 

Wakilan wannan Ƙungiya ta ‘Coalition of Northern Groups (CNG)’ na cikin wannan tattaunawa da aka yi, bisa wakilcin shugaban kwamitin amintattu na Ƙungiyar, Nastura Ashiru Shariff; shugaban kwamitin tsaro na ƙungiyar, Alhaji Bashir Yusuf; Alhaji Ibrahim Ahmed Katsina; Janar Sarkin Yaki Bello, Ambasada Buhari Bala da Janar Sa’ad Abubakar.

Zamfara
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Zamfara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo
  • Sulaiman
    Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

MASU ALAKA

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
Labarai

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Next Post
Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano

Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano

LABARAI MASU NASABA

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.