ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Zamfara Da Katsina Sun Gana Da Ministan Tsaro Da Ribaɗu

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal da takwaransa na jihar Katsina Dikko Umar Raɗɗa sun yi wata ganawar sirri da Ministan tsar, Badaru Abubakar da mai bai wa shugaba ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribaɗu.

 

Waɗannan ganawa guda biyu sun gudana ne a jiya Talata a ma’aikatar tsaro ta tarayya da kuma ofishin mai bai wa shugaban ƙasan shawara kan harkokin tsaro.

ADVERTISEMENT
  • Za Mu Fara Kamen Mabarata A Abuja – Wike
  • An Watsa Shirin Bidiyo Zagaye Na 3 Mai Taken “Bayanan Magabata Da Xi Jinping Yake So” A Rasha

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau, ya bayyana cewa, taron ya yi zuzzurfan tattaunawa game da shawarwarin da haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙungiyoyin Arewa ta ‘Coalition of Northern Groups (CNG)’ ta bayar.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

Sanarwar ta yi ƙarin haske da cewa, haɗaɗɗiyar ƙungiyar ‘yan Arewar ta gudanar da wani taro ne na kwana biyu a Abuja a ranar 23 ga watan Janairun 2024, wanda tsohon shugaban ƙasa, Janar Abdussalami Abubakar ya shugabanta.

 

Sanarwar ta Idris ta ce, “jiya Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara da Gwamna Dikko Umar Raɗɗa na jihar Katsina sun gana da Ministan tsaro Badaru Abubakar a ma’aikatar tsaro da ke Abuja.

 

“Gwamnonin sun tattauna muhimman batutuwan da suka shafi tsaro a jihohin biyu, tare da samar da hanyoyin bi, bisa haɗin gwiwa da ma’aikatar tsaron don magance matsalar.

 

“Bayan zaman da ya gudana ma’aikatar rsaron, sai Gwamnonin biyu tare da Ministan tsaron, suka wuce zuwa ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro don gudanar da wani zaman na musamman.

 

“A wannan zaman tattaunawar ne suka amince da shawarwarin da aka bayar da wancan taro, wanda haɗaɗɗiyar ƙungiyar ‘yan Arewar ta bayar.

 

“A cikin watan Janairun shekarar nan ne haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙungiyoyin Arewa ta gabatar da wani taron tattaunawa, wanda tsohon shugaban ƙasa, Janar Abdussalami Abubakar, tare da halartar wasu fitattun masu ruwa da tsaki daga yankin Arewacin ƙasar nan.

 

“Aiwatar da waɗannan shawawarin da wannan kwamiti na tsaro ya bayar, zai taimaka matuƙa wajen magance wannan tsalar tsaro mai rikitarwa da ta addabi Arewa Nijeriya.

 

“Wannan na cikin dabarbaru da haɗin gwiwar da waɗannan gwamnoni na Zamfara da Katsina suke bi don ganin sun kawo ƙarshen ‘yan bindiga a jihohin su.

 

Wakilan wannan Ƙungiya ta ‘Coalition of Northern Groups (CNG)’ na cikin wannan tattaunawa da aka yi, bisa wakilcin shugaban kwamitin amintattu na Ƙungiyar, Nastura Ashiru Shariff; shugaban kwamitin tsaro na ƙungiyar, Alhaji Bashir Yusuf; Alhaji Ibrahim Ahmed Katsina; Janar Sarkin Yaki Bello, Ambasada Buhari Bala da Janar Sa’ad Abubakar.

Zamfara
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
Zamfara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Zamfara
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Zamfara
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Zamfara
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Next Post
Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano

Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano

LABARAI MASU NASABA

Zamfara

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Zamfara

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.