• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Gidan Aure (4) Mijina Ba Ya Kula ‘Ya`yana

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
aure

Assalamu alaikum masu karatu barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon a cikin shirin namu mai farin jini da albarka na Uwargida Sarautar Mata.

A yau shafin na mu zai ci gaba da kawo muku matsalolin gidan aure da yadda za a magance su: Abin da za mu tattauna a yau shi ne batun kula ‘ya`ya. Tabbas kowace uwa tana so ta ga yadda mijinta yake son ‘ya’yan da ta haifa masa. Ko ba ma shi da ya haife su ba, uwa takan ji dadi idan mutane suka so mata ‘ya’ya, shi ya sa ma aka ce “maso uwa ya so ‘ya’yanta”, to ina ga uban da kuma ya haifo su? Sai dai uwargida, yana da kyau ki sani, kafin ki zargi maigida rashin kula miki da ‘ya’ya ke ya kamata ki koya wa ‘ya’yanki yadda za su kula da babansu.

  • Sirrin Zaman Lafiyar Da Ake Mora A Jihar Nasarawa –Kakakin Gwamnan Jihar
  • Na Sha Duka Kafin A Amince In Shiga Harkar Fim – Khadija Mai Numfashi

Da safe ki koya musu gaishe shi da zarar ya fita dama kamar jiran sa suke su je su gaishe shi, haka da yamma yana dawowa ki koya musu yadda za su tare shi idan mai mota ne da zarar sun ji shigowarsa su je su jira ya yi fakin su bude masa kofa, su yi masa sannu da zuwa, idan akwai kaya su debo.

Sannan ki koya musu sanin matsayinsa a wajensu da kuma yadda za su girmama shi fiye da kowane mutum a duniya, da yadda za su rika jin tsoran duk wani abin da zai bata masa rai, sannan kuma su so duk wani abin da zai faranta masa rai. Idan kika koya wa ‘ya’yanki haka za ki ga yadda babansu zai rika son su yana jan su a jikinsa.

Yaya tsaftarsu? Ya kamata ki kasance mai tsaftace ya’yanki a koda yaushe wanka wanki guga, matan kuma kitso akai-akai, maza aski idan gashi ya fito. Sannan ki hana ‘ya’yanki bata kayansu idan suna kanana, idan za su ci abinci ki cire musu kaya saboda kar ya baci, bayan sungama sai ki maida musu kaya.

LABARAI MASU NASABA

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Dawa yaran suke harka? Ya kamata ki zama mai sa ido akan ‘ya’yanki ki san dawa suke hulda, da wadanne irin abokai suke mu’amalarsu?.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)
Uwargida Sarautar Mata

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)
Uwargida Sarautar Mata

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

October 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?
Uwargida Sarautar Mata

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Next Post
Aure

Gimbiyoyin Kannywood (4)

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.