• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayakan Boko Haram 443 Sun Mika Wuya Yayin Da ISWAP Ta Kashe Musu Sama Da Mutum 300

by Sadiq
3 years ago
Boko Haram

Akalla wasu karin ‘yan ta’addan Boko Haram 443 da ne suka tsere daga munanan hare-haren da mayakan ISWAP suka yi a Jihar Borno na tsawon mako guda, sun mika wuya ga sojoji.

Wannan dai na zuwa ne yayin da adadin wadanda suka mutu a bangaren Boko Haram bayan harin na ISWAP ya kai 300.

  • Bita Da Karashen Darasi A Kan Kyawon Cika Alkawari Na Annabi (SAW)
  • Saudiyya Da Iran Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dawo Da Huldar Jakadanci Tare Da Sake Bude Ofisoshin Jakadanci A Tsakaninsu

Kimanin ‘yan Boko Haram 223 ne suka mika wuya ga dakarun rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa (MNJTF) a Diffa da Gueskerou, a Jamhuriyar Nijar tsakanin 7 zuwa 10 ga watan Maris, 2023.

Wasu ‘yan ta’addan Boko Haram 220 ne suka mika wuya ga dakarun Operation Hadin Kai a ranar 10 ga watan Maris, inda suka bayyana cewa fadan da ake yi tsakanin bangarorin biyu ya tilasta musu tserewa zuwa wasu wurare masu tsaro.

Tun daga ranar 27 ga Fabrairu, 2023, ‘yan Boko Haram sun tsere daga matsugunansu a sakamakon munanan hare-haren da aka kai wa kungiyar a Gaizuwa, wanda aka fi sani da Mantari, Gabchari, Kashimiri, Maimusari a Bama, Yale a Konduga da Magumeri.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

A daya daga cikin hare-haren da wasu fitattun kwamandojin ISWAP guda uku da suka hada da Malam Abubakar Maina, Qaed Malam Dahiru, da Qaed Mallam Dahiru suka jagoranta a Guzamala, an kawar da mayakan Boko Haram sama da 200 da suka hada da mata da yaransu.

An ci gaba da kai farmaki kan kungiyar a ranar 8 ga watan Maris, 2023, lokacin da aka kashe fiye da 100 daga cikinsu a gefen Baga, Marte da Dikwa.

A cewar Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya a yankin tafkin Chadi, gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta hannun hukumar yada labaranta da hulda da jama’a, an gudanar da makon ne da tarwatsa wasu kungiyoyin ‘yan ta’adda da suka bar dajin Sambisa zuwa tafkin. Chadi a bangaren Nijar.

Har ila yau, Darakta, ayyukan yada labarai na tsaro na hedikwatar tsaron Nijeriya, Manjo-Janar Musa Danmadami, ya bayyana adadin ‘yan Boko Haram da suka mika wuya a cikin makonni biyu da suka gabata zuwa 1,332. Wannan adadi ya karu a cikin kwanaki masu zuwa.

A yanzu dai za a ga yadda gwabzawar da ke tsakanin kungiyar Boko Haram da takwarorinta na baya-bayan nan a yakin ISWAP, za ta yi tasiri a yakin da ake yi na tsawon shekaru fiye da goma ana zubar da jini a yankin tafkin Chadi na Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Manyan Labarai

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Yadda Amurka Ta Kara Sanyawa Kamfanonin Sin Takunkumi

Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Yadda Amurka Ta Kara Sanyawa Kamfanonin Sin Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.