ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayakan Boko Haram 443 Sun Mika Wuya Yayin Da ISWAP Ta Kashe Musu Sama Da Mutum 300

by Sadiq
3 years ago
Boko Haram

Akalla wasu karin ‘yan ta’addan Boko Haram 443 da ne suka tsere daga munanan hare-haren da mayakan ISWAP suka yi a Jihar Borno na tsawon mako guda, sun mika wuya ga sojoji.

Wannan dai na zuwa ne yayin da adadin wadanda suka mutu a bangaren Boko Haram bayan harin na ISWAP ya kai 300.

  • Bita Da Karashen Darasi A Kan Kyawon Cika Alkawari Na Annabi (SAW)
  • Saudiyya Da Iran Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dawo Da Huldar Jakadanci Tare Da Sake Bude Ofisoshin Jakadanci A Tsakaninsu

Kimanin ‘yan Boko Haram 223 ne suka mika wuya ga dakarun rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa (MNJTF) a Diffa da Gueskerou, a Jamhuriyar Nijar tsakanin 7 zuwa 10 ga watan Maris, 2023.

ADVERTISEMENT

Wasu ‘yan ta’addan Boko Haram 220 ne suka mika wuya ga dakarun Operation Hadin Kai a ranar 10 ga watan Maris, inda suka bayyana cewa fadan da ake yi tsakanin bangarorin biyu ya tilasta musu tserewa zuwa wasu wurare masu tsaro.

Tun daga ranar 27 ga Fabrairu, 2023, ‘yan Boko Haram sun tsere daga matsugunansu a sakamakon munanan hare-haren da aka kai wa kungiyar a Gaizuwa, wanda aka fi sani da Mantari, Gabchari, Kashimiri, Maimusari a Bama, Yale a Konduga da Magumeri.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A daya daga cikin hare-haren da wasu fitattun kwamandojin ISWAP guda uku da suka hada da Malam Abubakar Maina, Qaed Malam Dahiru, da Qaed Mallam Dahiru suka jagoranta a Guzamala, an kawar da mayakan Boko Haram sama da 200 da suka hada da mata da yaransu.

An ci gaba da kai farmaki kan kungiyar a ranar 8 ga watan Maris, 2023, lokacin da aka kashe fiye da 100 daga cikinsu a gefen Baga, Marte da Dikwa.

A cewar Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya a yankin tafkin Chadi, gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta hannun hukumar yada labaranta da hulda da jama’a, an gudanar da makon ne da tarwatsa wasu kungiyoyin ‘yan ta’adda da suka bar dajin Sambisa zuwa tafkin. Chadi a bangaren Nijar.

Har ila yau, Darakta, ayyukan yada labarai na tsaro na hedikwatar tsaron Nijeriya, Manjo-Janar Musa Danmadami, ya bayyana adadin ‘yan Boko Haram da suka mika wuya a cikin makonni biyu da suka gabata zuwa 1,332. Wannan adadi ya karu a cikin kwanaki masu zuwa.

A yanzu dai za a ga yadda gwabzawar da ke tsakanin kungiyar Boko Haram da takwarorinta na baya-bayan nan a yakin ISWAP, za ta yi tasiri a yakin da ake yi na tsawon shekaru fiye da goma ana zubar da jini a yankin tafkin Chadi na Nijeriya.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Yadda Amurka Ta Kara Sanyawa Kamfanonin Sin Takunkumi

Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Yadda Amurka Ta Kara Sanyawa Kamfanonin Sin Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.