• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ficewar Kasashen Sahel Daga Ecowas Ke Nufi?

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Me Ficewar Kasashen Sahel Daga Ecowas Ke Nufi?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi, 15 ga watan Disamban 2024 ne kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka, ECOWAS, ta amince da ficewar kasashen Sahel wato Nijar, Mali da Burkina Faso daga kungiyar.

Kungiyar ta bayar da sanarwar ne a karshen taron koli da ta yi a Abuja, Babban Birnin Nijeriya, inda ta ce daga ranar 29 ga watan Janairun shekara mai kamawa kasashen uku za su daina zama mambobin kungiyar.

  • Babban Aikin “Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana A Wajen Da Ake Kiwon Kifi” A Sin Ya Fara Aiki
  • Gwamnatin Katsina Ta Sha Alwashin Dakile Rikici Tsakanin Makiyaya Da Manoma

A farkon shekarar nan ne kasashen uku suka fitar da sanarwar hadin gwiwa ta bukatar ficewa, saboda a cewarsu kungiyar ta kasa magance matsalolin tsaro na kungiyoyi masu ikirarin jihadi da ke da alaka da ISIS da al-Kaeda da ke neman wargaza yankin.

Me ya sa ECOWAS ta amince?

BBC ta yi tattauna dakta El Haroon Muhammad, masani a harkar diflomasiyya da dabarun raya kasashe, ya ce dole ce ta sa Ecowas daukar matakin saboda babu alama cewa wadannan kasashen za su dawo cikin kungiyar.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

”Yadda suka rungumi kasar Rasha, yadda suke mu’amala da Turkiyya da Iran, suka kawo musu tsare-tsare da zai kawo ci gaban kasashen da bunkasar tattalin arzikinsu, dole ne ECOWAS ta dubi wannan matsayin” a cewar shi.

A taron da kungiyar ta yi ranar lahadi, ta kuma ce kofa a bude take ga kasashen Sahel din nan da watanni shida idan sun sauya shawara suna so su koma cikin kungiyar.

Dakta El Haroon ya ce sake ba su damar ba zai yi amfani ba saboda kasashen na duba amfanin kansu ne.

“Abin da zai kara lalata al’amarin shi ne yadda shugaban Nijeriya ya zama babban aminin Faransa, wanda ya ce hakan zai kara firgita kasashen su janye jikinsu.”

Wace irin riba ficewar kasashen Sahel ukun zai yi ga ECOWAS?

Dakta El Haroon Muhammad ya ce babu wata riba da kungiyar ECOWAS za ta ci, illa ta kara faduwa.

”Idan aka dauki tarihin kungiyar ta ECOWAS, yau wajen shekara 40, duk abubuwan da ta sa a gaba za ta yi ba ta yi su ba, idan tafiya ta kama dan mamban kasar zai je makwabciyar kasar, irin wahalar da zai sha a hannun jami’an tsaro, kwastam da sojoji sai ya yi wayyo Allah.”

Ya kuma ce kasashen kungiyar sun kasa yin kudin kansu, sun kasa inganta kasuwanci, manufarsu na kawo habakar tattalin arziki da magance talauci duk sun gaza.

Wace irin riba kasashe ukun za su ci bayan ficewarsu?

Masanin harkar diflomasiyyar da dabarun raya kasashe Dakta Elharoon Muhammad ya ce janye jikin kasashen uku daga kungiyar shi ne alheri a gare su kuma akwai riba da yawa wadanda sun ma fara ganin wasu daga ciki.

”Ga riba nan suna ci, irin tatsar arzikin da Faransa ta yi musu, ta rike musu wuya, da suka kori Faransa ga shi nan suna ta walwala da su na bunkasa suna kuma fadada harkokinsu da kasashen waje. Su ke cin riba,” inj i Dakta El-Haroon.

Ya kuma ce dole ne kasashen sun yi haka saboda sun dade kasar Faransa na bautar da su, suna daga cikin kasashen da su ka fi koma baya a duniya, kuma yin haka shi ne mafi alheri a gare su.

”Tsakanin lokacin da kasashen suka kai ruwa rana da Faransa zuwa yanzu an ga sauye-sauyen da suka faru a kasashen.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kofin Duniya: FIFA Ta Fitar Da Yadda Za A Samu Gurbin Zuwa Amurka

Next Post

Bukukuwan Kirismeti: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Ranar 25 ga Disamba, 26, 1 ga Janairu Ranar Hutu

Related

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato
Tsaro

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

4 hours ago
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

5 hours ago
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

7 hours ago
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
Labarai

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

8 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

9 hours ago
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU
Labarai

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

9 hours ago
Next Post
Sahel

Bukukuwan Kirismeti: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Ranar 25 ga Disamba, 26, 1 ga Janairu Ranar Hutu

LABARAI MASU NASABA

A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.