• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ficewar Kasashen Sahel Daga Ecowas Ke Nufi?

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Me Ficewar Kasashen Sahel Daga Ecowas Ke Nufi?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi, 15 ga watan Disamban 2024 ne kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka, ECOWAS, ta amince da ficewar kasashen Sahel wato Nijar, Mali da Burkina Faso daga kungiyar.

Kungiyar ta bayar da sanarwar ne a karshen taron koli da ta yi a Abuja, Babban Birnin Nijeriya, inda ta ce daga ranar 29 ga watan Janairun shekara mai kamawa kasashen uku za su daina zama mambobin kungiyar.

  • Babban Aikin “Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana A Wajen Da Ake Kiwon Kifi” A Sin Ya Fara Aiki
  • Gwamnatin Katsina Ta Sha Alwashin Dakile Rikici Tsakanin Makiyaya Da Manoma

A farkon shekarar nan ne kasashen uku suka fitar da sanarwar hadin gwiwa ta bukatar ficewa, saboda a cewarsu kungiyar ta kasa magance matsalolin tsaro na kungiyoyi masu ikirarin jihadi da ke da alaka da ISIS da al-Kaeda da ke neman wargaza yankin.

Me ya sa ECOWAS ta amince?

BBC ta yi tattauna dakta El Haroon Muhammad, masani a harkar diflomasiyya da dabarun raya kasashe, ya ce dole ce ta sa Ecowas daukar matakin saboda babu alama cewa wadannan kasashen za su dawo cikin kungiyar.

Labarai Masu Nasaba

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

”Yadda suka rungumi kasar Rasha, yadda suke mu’amala da Turkiyya da Iran, suka kawo musu tsare-tsare da zai kawo ci gaban kasashen da bunkasar tattalin arzikinsu, dole ne ECOWAS ta dubi wannan matsayin” a cewar shi.

A taron da kungiyar ta yi ranar lahadi, ta kuma ce kofa a bude take ga kasashen Sahel din nan da watanni shida idan sun sauya shawara suna so su koma cikin kungiyar.

Dakta El Haroon ya ce sake ba su damar ba zai yi amfani ba saboda kasashen na duba amfanin kansu ne.

“Abin da zai kara lalata al’amarin shi ne yadda shugaban Nijeriya ya zama babban aminin Faransa, wanda ya ce hakan zai kara firgita kasashen su janye jikinsu.”

Wace irin riba ficewar kasashen Sahel ukun zai yi ga ECOWAS?

Dakta El Haroon Muhammad ya ce babu wata riba da kungiyar ECOWAS za ta ci, illa ta kara faduwa.

”Idan aka dauki tarihin kungiyar ta ECOWAS, yau wajen shekara 40, duk abubuwan da ta sa a gaba za ta yi ba ta yi su ba, idan tafiya ta kama dan mamban kasar zai je makwabciyar kasar, irin wahalar da zai sha a hannun jami’an tsaro, kwastam da sojoji sai ya yi wayyo Allah.”

Ya kuma ce kasashen kungiyar sun kasa yin kudin kansu, sun kasa inganta kasuwanci, manufarsu na kawo habakar tattalin arziki da magance talauci duk sun gaza.

Wace irin riba kasashe ukun za su ci bayan ficewarsu?

Masanin harkar diflomasiyyar da dabarun raya kasashe Dakta Elharoon Muhammad ya ce janye jikin kasashen uku daga kungiyar shi ne alheri a gare su kuma akwai riba da yawa wadanda sun ma fara ganin wasu daga ciki.

”Ga riba nan suna ci, irin tatsar arzikin da Faransa ta yi musu, ta rike musu wuya, da suka kori Faransa ga shi nan suna ta walwala da su na bunkasa suna kuma fadada harkokinsu da kasashen waje. Su ke cin riba,” inj i Dakta El-Haroon.

Ya kuma ce dole ne kasashen sun yi haka saboda sun dade kasar Faransa na bautar da su, suna daga cikin kasashen da su ka fi koma baya a duniya, kuma yin haka shi ne mafi alheri a gare su.

”Tsakanin lokacin da kasashen suka kai ruwa rana da Faransa zuwa yanzu an ga sauye-sauyen da suka faru a kasashen.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kofin Duniya: FIFA Ta Fitar Da Yadda Za A Samu Gurbin Zuwa Amurka

Next Post

Bukukuwan Kirismeti: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Ranar 25 ga Disamba, 26, 1 ga Janairu Ranar Hutu

Related

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara
Labarai

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

5 hours ago
APC
Labarai

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

6 hours ago
Tinubu
Labarai

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

9 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

10 hours ago
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

13 hours ago
Next Post
Sahel

Bukukuwan Kirismeti: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Ranar 25 ga Disamba, 26, 1 ga Janairu Ranar Hutu

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.