ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ficewar Kasashen Sahel Daga Ecowas Ke Nufi?

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 years ago
Sahel

A ranar Lahadi, 15 ga watan Disamban 2024 ne kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka, ECOWAS, ta amince da ficewar kasashen Sahel wato Nijar, Mali da Burkina Faso daga kungiyar.

Kungiyar ta bayar da sanarwar ne a karshen taron koli da ta yi a Abuja, Babban Birnin Nijeriya, inda ta ce daga ranar 29 ga watan Janairun shekara mai kamawa kasashen uku za su daina zama mambobin kungiyar.

  • Babban Aikin “Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana A Wajen Da Ake Kiwon Kifi” A Sin Ya Fara Aiki
  • Gwamnatin Katsina Ta Sha Alwashin Dakile Rikici Tsakanin Makiyaya Da Manoma

A farkon shekarar nan ne kasashen uku suka fitar da sanarwar hadin gwiwa ta bukatar ficewa, saboda a cewarsu kungiyar ta kasa magance matsalolin tsaro na kungiyoyi masu ikirarin jihadi da ke da alaka da ISIS da al-Kaeda da ke neman wargaza yankin.

ADVERTISEMENT

Me ya sa ECOWAS ta amince?

BBC ta yi tattauna dakta El Haroon Muhammad, masani a harkar diflomasiyya da dabarun raya kasashe, ya ce dole ce ta sa Ecowas daukar matakin saboda babu alama cewa wadannan kasashen za su dawo cikin kungiyar.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Ya Ci Gaba Da Tafiya A Turba Mai Kyau Yayin Da Masana’antun Manyan Fasaha Da Cinikayyar Ketare Ke Habaka

An Raba Keken Adaidaita 238 Domin Kai Marasa Lafiya Asibitoci A Katsina

”Yadda suka rungumi kasar Rasha, yadda suke mu’amala da Turkiyya da Iran, suka kawo musu tsare-tsare da zai kawo ci gaban kasashen da bunkasar tattalin arzikinsu, dole ne ECOWAS ta dubi wannan matsayin” a cewar shi.

A taron da kungiyar ta yi ranar lahadi, ta kuma ce kofa a bude take ga kasashen Sahel din nan da watanni shida idan sun sauya shawara suna so su koma cikin kungiyar.

Dakta El Haroon ya ce sake ba su damar ba zai yi amfani ba saboda kasashen na duba amfanin kansu ne.

“Abin da zai kara lalata al’amarin shi ne yadda shugaban Nijeriya ya zama babban aminin Faransa, wanda ya ce hakan zai kara firgita kasashen su janye jikinsu.”

Wace irin riba ficewar kasashen Sahel ukun zai yi ga ECOWAS?

Dakta El Haroon Muhammad ya ce babu wata riba da kungiyar ECOWAS za ta ci, illa ta kara faduwa.

”Idan aka dauki tarihin kungiyar ta ECOWAS, yau wajen shekara 40, duk abubuwan da ta sa a gaba za ta yi ba ta yi su ba, idan tafiya ta kama dan mamban kasar zai je makwabciyar kasar, irin wahalar da zai sha a hannun jami’an tsaro, kwastam da sojoji sai ya yi wayyo Allah.”

Ya kuma ce kasashen kungiyar sun kasa yin kudin kansu, sun kasa inganta kasuwanci, manufarsu na kawo habakar tattalin arziki da magance talauci duk sun gaza.

Wace irin riba kasashe ukun za su ci bayan ficewarsu?

Masanin harkar diflomasiyyar da dabarun raya kasashe Dakta Elharoon Muhammad ya ce janye jikin kasashen uku daga kungiyar shi ne alheri a gare su kuma akwai riba da yawa wadanda sun ma fara ganin wasu daga ciki.

”Ga riba nan suna ci, irin tatsar arzikin da Faransa ta yi musu, ta rike musu wuya, da suka kori Faransa ga shi nan suna ta walwala da su na bunkasa suna kuma fadada harkokinsu da kasashen waje. Su ke cin riba,” inj i Dakta El-Haroon.

Ya kuma ce dole ne kasashen sun yi haka saboda sun dade kasar Faransa na bautar da su, suna daga cikin kasashen da su ka fi koma baya a duniya, kuma yin haka shi ne mafi alheri a gare su.

”Tsakanin lokacin da kasashen suka kai ruwa rana da Faransa zuwa yanzu an ga sauye-sauyen da suka faru a kasashen.”

Sahel
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Sahel
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Bude Taron Kasa Da Kasa Karo Na 5 Dangane Da Tsarin Cin Gajiyar Fasahar Taurarin Dan Adam Na Beidou
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Nasarar Harba Taurarin Dan Adam 10 Ta Amfani Da Rokar Zhuque-2E
  • Sulaiman
    Tattalin Arzikin Sin Ya Ci Gaba Da Tafiya A Turba Mai Kyau Yayin Da Masana’antun Manyan Fasaha Da Cinikayyar Ketare Ke Habaka
  • Sulaiman
    An Raba Keken Adaidaita 238 Domin Kai Marasa Lafiya Asibitoci A Katsina

MASU ALAKA

Tattalin Arzikin Sin Ya Ci Gaba Da Tafiya A Turba Mai Kyau Yayin Da Masana’antun Manyan Fasaha Da Cinikayyar Ketare Ke Habaka
Labarai

Tattalin Arzikin Sin Ya Ci Gaba Da Tafiya A Turba Mai Kyau Yayin Da Masana’antun Manyan Fasaha Da Cinikayyar Ketare Ke Habaka

September 15, 2026
Gwamnatin Katsina
Manyan Labarai

An Raba Keken Adaidaita 238 Domin Kai Marasa Lafiya Asibitoci A Katsina

September 15, 2026
'yansanda
Labarai

Gargaɗi: ‘Yansanda Sun Gano Shirin Kai Hare-hare A Makarantu Da Wuraren Ibada

September 15, 2026
Next Post
Sahel

Bukukuwan Kirismeti: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Ranar 25 ga Disamba, 26, 1 ga Janairu Ranar Hutu

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Kasa Da Kasa Karo Na 5 Dangane Da Tsarin Cin Gajiyar Fasahar Taurarin Dan Adam Na Beidou

An Bude Taron Kasa Da Kasa Karo Na 5 Dangane Da Tsarin Cin Gajiyar Fasahar Taurarin Dan Adam Na Beidou

September 15, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Harba Taurarin Dan Adam 10 Ta Amfani Da Rokar  Zhuque-2E

Sin Ta Yi Nasarar Harba Taurarin Dan Adam 10 Ta Amfani Da Rokar Zhuque-2E

September 15, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Ci Gaba Da Tafiya A Turba Mai Kyau Yayin Da Masana’antun Manyan Fasaha Da Cinikayyar Ketare Ke Habaka

Tattalin Arzikin Sin Ya Ci Gaba Da Tafiya A Turba Mai Kyau Yayin Da Masana’antun Manyan Fasaha Da Cinikayyar Ketare Ke Habaka

September 15, 2026
Gwamnatin Katsina

An Raba Keken Adaidaita 238 Domin Kai Marasa Lafiya Asibitoci A Katsina

September 15, 2026
Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS

Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS

September 15, 2026
Tsoffin Shugabannin Hukumar NFF Sun Buƙaci A Naɗa Kwamiti Domin Warware Matsalolin Hukumar

Tsoffin Shugabannin Hukumar NFF Sun Buƙaci A Naɗa Kwamiti Domin Warware Matsalolin Hukumar

September 15, 2026
Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe

Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe

September 15, 2026
NFF Ta Dakatar Da Alkalin Wasa Sakamakon Kwallon Da Ya Hana A Wasan Doma United Da Enyimba

NFF Ta Dakatar Da Alkalin Wasa Sakamakon Kwallon Da Ya Hana A Wasan Doma United Da Enyimba

September 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da Zurfafa Hadin Kai A Babban Taron IAEA

Sin Ta Yi Kira Da Zurfafa Hadin Kai A Babban Taron IAEA

September 15, 2026
'yansanda

Gargaɗi: ‘Yansanda Sun Gano Shirin Kai Hare-hare A Makarantu Da Wuraren Ibada

September 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.