• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ke Kawo Zargi Tsakanin Wadanda Suke Gab Da Su Yi Aure?

by Bilkisu Tijjani
8 months ago
in Labarai
0
Me Ke Kawo Zargi Tsakanin Wadanda Suke Gab Da Su Yi Aure?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin Taskira shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma. Tsokacimmu na yau zai magana ne game da zargi da yake shiga tsakanin mutum biyu wadanda suka kusa aure.

Me ke kawo wannan zargi?

Fa’iza Musa

Abin da nake ganin yana kawo zargi shi ne, farko dai ni gaskiya ina ganin rashin sani addini da rashin sanin meye shi hukuncin zargin, domin in mutum ya san addini gwargwado da kuma hukuncin zargi da kuma hukuncin haramcin zargi a Musulunci zai yi duk abin da zai yi wajen kiyaye shi tun da kin ga kafin ka je ka ce kana son mutum ko Annabi ma ya fada mana cewa mu zabi me addini, cikin zamantakewarmu in mace ce ta zabi namijin mai addini shima kuma ya zabi mace mai addini daidai gwargwado domin zaman takewa na yau da kullum da kuma tarbiyyar ‘ya’ya, matukar ya zabi mai addini ko ta zabi mai addini tun kafin aure zai zamanto akwai takaitatcan zargi a tsakaninsu koma a ce ya zamanto babu zargin, saboda in na yarda dake na yarda da addininki na yarda da imaninki ba zai zamanto ina zarginki akan kome ba tun da gwargwado zan yi tunanin kina tsoran Allah duk abin da za ka yi kana yin sa domin Allah kuma duk abin da zaka yi ba za ka yi shi don ka cutar da wani ko ka cutar da kanka ba.

  • An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122
  • Netanyahu Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Zargin Rashawa

Sannan na biyu ko na uku abin da yake kara janyo tsargi tsakanin ma’aurata shi ne karya, su sa karya a cikin lamarinsu su zamanto makaryata don yana ganin sai ya yi karya za ta so shi, ko kuma ita ta zamanto makaryaciya ko wani abin ko kuma mai son abin duniya ko wani abin shima wannan ya kan iya jawo zargi ko wani abin saboda zai rinka ganin kamar ta raina abin da yake da shi, kila hankalinta ba a kanshi kadai yake ba.

Labarai Masu Nasaba

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

 

Sannan na uku kuma shi ne, yawan mu’amala da mutane da yawa, ya zamanto in kina tare da namiji ki ga yana mu’amala da mutane da yawa wato jinsin da ba nashi ba da yawa ko kuna tare ko kuna hira ko wani abu, ya zamanto kuna tare da shi yana yawon mu’amala da mata ko wani abu haka wanda de suke a tsammaninki ba muharramansa ba shima wannan yana kawo zargi to ya kamata duk wadanda za su yi aure a tsakanin mace da namiji koda a ce suna mu’amala da wasu daban a wajen jinsin daba nasu ba ya kasance duk lokacin da suke tare su kan dan takaitawa saboda kin ga wani namijin dan kasuwa ne ba yadda za’a yi a ce ba zai yi mu’amala da mata ba to lokacin da yake mu’amala da matan ya kasance ya sanar da ita da suwa yake yi ko kuma ma ya takaita lokacin ya rinka samun wani lokaci na kasuwancinshi shi da kuma lokaci na ita wacce zai aura koda bai aure ta ba shima a ganina in ya zamanto koda yaushe ne sai suna tare ko ita tana kasuwanci ko ita ma’aikaciyace tana mu’amala da maza yakasance duk lokacin da za ta yi lokacin wanda za ta aura daban lokacin da za ta yi mu’amala da abokan kasuwancinta daban.

Sai kuma shine abin da nake ganin yafi kome ma kawo zargi shi ne ma’aurata dayansu ya zamo mai magana da batsa duk maganar da za su yi tsakanin shi da wacce zai aura kai koda bayan ya aure ta ne ya zamanto da kamun kai sannan ya zamo yana furta maganganu daba za su zubar masa da mutunci ba, maganar data halatta maganar da ta zamto ba ta sabawa shari’ar Muslunci ba, wani lokaci za ki ga ma’auratanmu musamman samari da ‘yan mata wadanda kansu yake fuzga za ki ga don ina ganin za ka aure ni ko za ki aureni ina da damar in miki kowace irin magana to za ki ga saboda ina ganin kamar muna da kusanci wannan kuma ba daidai bane tsakanin ma’aurata wanda za su yi aure kai koda kun yi aure, akwai kalmomin da ya kamata mutum ya rinka furtawa mutum ba sai ya furta ba saboda su kan iya zubar misa da mutumci sannan kuma su kan iya sa zargi a tsakaninsu ya zamanto duk kalmar da za ka furta kalma ce mai kyau wanda shari’a ta yarda da shi sannan kuma magana ce wanda kunne zai dauka ba batsa bane ba, wanda ko a Musulunci haramun ne . Allah ya sa mu dace.

 

Bilkisu Maharazu

Abin da ke kawo zargi tsakanin wadanda suke gab da sun yi aure shi ne: Na farko akwai zafin kishi wanda shi wannan zafin kishin idan ya yi yawa shi ne yake kawo zargi tsanin ma’aurata har ya kan kai da rabuwa a tsakanin su kwata-kwata, saboda idan ya yi yawa sai ki ga kullum ana ta fadace-fadace a tsakaninsu.

Na biyu akwai rashin fahimta juna saboda ba a yi auren aka zauna ba ballantana  a fahimci juna, amma ya kamata ku kasance masu fahimta juna, tun kafin ku yi aure, to da zarar an fahimci juna, to sai komai ya tafi daidai yadda ya kamata, ba tare da an samu matsala ba, sai dai dan abin da ba za a rasa ba, na yau da kullum wanda dama shi aure haka yake ga kowa, masu magana na cewa zo mu zauna zo mu saba. Muna fatan alkhairi da duk masu shirin yin aure da wadanda suke ciki Allah ya zaunar da su lafiya.

 

Usman Sani

Haka na iya faruwa ne, saboda rashin fahimtar juna, rashin amincewa, ko kuma yayin da aka samu maganganun banza daga wasu mutane ko ‘yan uwa.

Saboda wasu za ku ga ana samun yawan gulmace-gulmace na mutane na kai kawo a tsakaninsu, sannan akwai shedan wanda dama shi ne ummul haba’isu, shike haddasa komai, shike sawa mutum wasuwasi yanzu haka wani na can yana yin kaza, shi ne ya hada ku ya sa maka zargi, daga nan sai ka fara ganin laifin dan uwanka, kana ganin kamar yana can yana cin amanarka. Haka nan, idan akwai al’amar rashin gaskiya a cikin al’amuran daya daga cikin ma’auratan, hakan na iya haifar da zargi, saboda zai rika ganin kamar dayan ma haka yake, saboda shi ya sa ba gaskiya yake ba.

 

Abdurrahman Tijjani

Gaskiya ni a ganina, babban dalili shi ne, shedan, saboda dama shi shedan duk wani abin alkhairi da za’a yi kokarin yi shi, kuma sai ya yi iya bakin kokarinsa ya ga ya bata wannan abin. To wannan shi ne babban masabbabin abin da yake kawo zargi tsakanin ma’aurata ko kuma wadanda suke gab da yin aure.

Da zarar mutum bai yi kokarin fin karfin zuciyarsa ba to gaskiya shedan zai yi kokarin mamaye ta, da zarar ka bari shedan ya yi nasara a kanka to fa al’amuranka sai abin da hali ya yi saboda duk abin da zuciyarka ta raya, haka za ka ga shi ne daidai a wajenka koda ba daidai bane. Allah ya sa mu dace.

 

Khadija Abdullahi

Ni a ganina, gaskiya abin da ke kawo zargi tsakanin wadanda suke gab da aure shi ne, so ya yi yawa, to shi ne sai ka rika ganin kamar wanda kake so yana tare da wata, ko shi ya rinka ganin kamar ta tana tare da wani, su rinka ganin a junansu kamar daya yana cin amanar daya.

Sannan kuma dama, shedan ne ke kawo irin wadannan wasiwasin, shi ya sa ake so mutum ya yi kokari ya fi karfin zuciyarsa, saboda kar shedan ya mamaye masa zuciya.

Idan kana son mutum to ka sa yarda a tsakaninku, koda wasa kar ka yi kokarin kawo kukwanto a tsakaninku, to idan kuka yi haka za ku ga babu wani kokwanto da zai rika shiga tsakaninku. Allah ya sa mu dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Zargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwankwaso, Donald Duke Da Obasanjo Sun Tattauna Batun Shugabanci A Nijeriya

Next Post

Saboda Isar Da Sako Nake Yin Shirin Manyan Mata Ba Domin Kudin Da Zan Samu Ba -Abdul Amart

Related

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

44 minutes ago
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
Labarai

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

9 hours ago
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja
Labarai

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

11 hours ago
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
Labarai

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

12 hours ago
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
Labarai

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

12 hours ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Labarai

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

14 hours ago
Next Post
Saboda Isar Da Sako Nake Yin Shirin Manyan Mata Ba Domin Kudin Da Zan Samu Ba -Abdul Amart

Saboda Isar Da Sako Nake Yin Shirin Manyan Mata Ba Domin Kudin Da Zan Samu Ba -Abdul Amart

LABARAI MASU NASABA

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.