• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ake Rubibin Wike A Siyasar Nijeriya?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Siyasa
0
Me Ya Sa Ake Rubibin Wike A Siyasar Nijeriya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan kammala zaben fitar da gwani na takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP ake ta samun zaman doya da manja a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar PDP.

Wani sabon rikici ya kunno kai a kan zabin dan takarar mataimakin shugaban kasa a Jam’iyyar PDP.

  • Bincikenmu: An Dade Da Hana Karuwanci A Neja, Amma Abin Ya Dau Sabon Salo
  • Da Hannun Amurka A Kuskuren Kai Harin Sojin Nijeriya Na 2017 A Borno — Bincike

Akwai rahotanni da suke cewa Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, yana barazanar ficewa daga PDP bayan da Atiku Abubakar ya zabi Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023.

Wadannan rahotannin ne ya sanya wasu ke ta kamun kafa a wajen Wike idan ya bar jam’iyyar PDP ya shiga jam’iyyarsu ganin irin tasirin da yake da shi a yankin kudu maso kudancin Nijeriya.

Wasu fitattu manyan jam’iyyar PDP sun fito suna kokarin cire wa dan takarar shugaban kasar zani a kasuwa, inda suke cewa bai kyauta ba da ya tsallake gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, wajen zaben abokin takarasa, alama ce ta yankan shakku cewa za su kunna wata wutar rikici, wadda idan ba a yi wa tubkar-hanci ba za ta cinye jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

A nasa bangaren, Gwamnan Jihar Benuwe, Samuel Ortom, a wata zantawa da ‘yan jarida ya ce sam-sam dan takarar shugaban kasar a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Ababukar, bai yi halacci ba da ya ki amincewa da Gwamna Wike a matsayin mataimakisa.

A hannu guda kuwa, wasu ‘yan takarar shugaban kasa da kusoshin wasu jam’iyyun hamayyar ke tururu zuwa wajen Wike, kuma ga dukkan alamu da nufin yin wuf da shi daga jam’iyyar PDP.

A kwanakin nan an ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ya kai wa Mista Wike ziyara.

An ga kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ziyarci gwamnann Ribas.

Haka kuma wasu gwamnonin APC sun gana da Wike.

Kafafen yada labarai dai da dama sun ruwaito cewa cikin gwamnonin sun hada da gwamnan Jihar Ekiti kuma shugaban kungiyar gwamnoni, Dakta Kayode Fayemi tare da gwamnan Legas da kuma na Ondo.

Sai dai babu wani abu da ya fito na dalili da kuma sakamakon tattaunawar tsakanin Wike da gwamnonin na APC, amma ba ya rasa nasaba da zaben 2023.

Baya ga wannan kuma, sai ga ‘yan tawayen APC wato su Yakubu Dogara da Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal sun kai wa Wike ziyara jim kadan bayan dawowarsa daga bulaguro a kasar waje.

Har Yakubu Dogara yake cewa Nijeriya na bukatar mutane irin su Wike don a gyarata.

A ranar Lahadi, 31 ga watan Yulin 2022, gwamnonin PDP sun kai wa Wike ziyara. Gwamnonin sun kai ziyarar ce kwana daya bayan da manyan ‘yan tawayen APC, suka Kai masa ziyara.

Gwamnonin da suka kai wa Wike ziyara, sun je ne tare da wasu tsoffin gwamnonin PDP, inda a ranar Lahadi suka gana da shi a asirce, a gidan Gwamnatin Jihar Ribas da ke Asokoro cikin garin Abuja.

Ba a san dai abin da suka tattauna ba. Amma kuma tabbas tattaunawar ba ta rasa nasaba da sabanin da ke kara tsanani tsakanin Wike da Atiku Abubakar.

Daga baya Wike ya ce Atiku ya yaudare shi, domin bayan kammala zaben, ya bi Wike har gida ya ba shi hakuri. Kuma ya ce shi zai dauka mataimakin takararsa.

Manyan PDP sun fara jin tsoron Wike tun bayan da gwamnonin APC uku daga kudu maso yamma suka kai masa ziyara.

Sai kuma ziyarar da Yakubu Dogara da Babachir Lawal suka kai masa a ranar Asabar.

Rahotanni dai da dama na nuna cewa Wike dai na cewa ba zai fita daga PDP ba, shi da jam’iyyar mutu-ka-raba.

Amma abun tambaya a nan wani irin tasiri Wike yake da shi haka har zama tamkar gwal?

Lallai wannan tambaya tana da amsa, idann aka duba irin tasirin da yake da shi a cikin harkokin siyasar Jihar Ribas da ma Nijeriya gaba daya za a ga cewa rasa irin Wike a cikin jam’iyya babban nakasu ne, domin yana da dimbin magoya baya, sannan yana iya amfani da kudinsa wajen gina jam’iyya da samun nasara a cikin siyasa.

Ya kasance wani bango da ake kallo a cikin harkokin siyasan kudancin Nijeriya da ke da tasiri wajen tsayawa kan akidarsa, wanda yake da wahalar taukwaruwa.

Tabbas Wike yana da matukar tasiri a cikin harkokin siyasar Nijeriya, musamman ma a cikin jam’iyyarsa ta PDP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023APCAtikuIfeanyi OkowaLPNNPPPDPSiyasaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana Sun Bukaci Mata Masu Aiki Su Rungumi Akidar Shayar Da Jariransu Nonon Uwa

Next Post

2023: Wata Kungiya Zata Yi Gangamin Tara Wa Atiku Gudunmawar Biliyan 1 Na Kamfen

Related

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

2 hours ago
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

2 days ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

2 days ago
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

3 days ago
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

4 days ago
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

5 days ago
Next Post
Atiku Ya Nada Dino Melaye Da Daniel Bwala A Matsayin Masu Magana da Yawunsa

2023: Wata Kungiya Zata Yi Gangamin Tara Wa Atiku Gudunmawar Biliyan 1 Na Kamfen

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.