ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ake Rubibin Wike A Siyasar Nijeriya?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Wike

Tun bayan kammala zaben fitar da gwani na takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP ake ta samun zaman doya da manja a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar PDP.

Wani sabon rikici ya kunno kai a kan zabin dan takarar mataimakin shugaban kasa a Jam’iyyar PDP.

  • Bincikenmu: An Dade Da Hana Karuwanci A Neja, Amma Abin Ya Dau Sabon Salo
  • Da Hannun Amurka A Kuskuren Kai Harin Sojin Nijeriya Na 2017 A Borno — Bincike

Akwai rahotanni da suke cewa Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, yana barazanar ficewa daga PDP bayan da Atiku Abubakar ya zabi Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023.

ADVERTISEMENT

Wadannan rahotannin ne ya sanya wasu ke ta kamun kafa a wajen Wike idan ya bar jam’iyyar PDP ya shiga jam’iyyarsu ganin irin tasirin da yake da shi a yankin kudu maso kudancin Nijeriya.

Wasu fitattu manyan jam’iyyar PDP sun fito suna kokarin cire wa dan takarar shugaban kasar zani a kasuwa, inda suke cewa bai kyauta ba da ya tsallake gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, wajen zaben abokin takarasa, alama ce ta yankan shakku cewa za su kunna wata wutar rikici, wadda idan ba a yi wa tubkar-hanci ba za ta cinye jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

A nasa bangaren, Gwamnan Jihar Benuwe, Samuel Ortom, a wata zantawa da ‘yan jarida ya ce sam-sam dan takarar shugaban kasar a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Ababukar, bai yi halacci ba da ya ki amincewa da Gwamna Wike a matsayin mataimakisa.

A hannu guda kuwa, wasu ‘yan takarar shugaban kasa da kusoshin wasu jam’iyyun hamayyar ke tururu zuwa wajen Wike, kuma ga dukkan alamu da nufin yin wuf da shi daga jam’iyyar PDP.

A kwanakin nan an ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ya kai wa Mista Wike ziyara.

An ga kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ziyarci gwamnann Ribas.

Haka kuma wasu gwamnonin APC sun gana da Wike.

Kafafen yada labarai dai da dama sun ruwaito cewa cikin gwamnonin sun hada da gwamnan Jihar Ekiti kuma shugaban kungiyar gwamnoni, Dakta Kayode Fayemi tare da gwamnan Legas da kuma na Ondo.

Sai dai babu wani abu da ya fito na dalili da kuma sakamakon tattaunawar tsakanin Wike da gwamnonin na APC, amma ba ya rasa nasaba da zaben 2023.

Baya ga wannan kuma, sai ga ‘yan tawayen APC wato su Yakubu Dogara da Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal sun kai wa Wike ziyara jim kadan bayan dawowarsa daga bulaguro a kasar waje.

Har Yakubu Dogara yake cewa Nijeriya na bukatar mutane irin su Wike don a gyarata.

A ranar Lahadi, 31 ga watan Yulin 2022, gwamnonin PDP sun kai wa Wike ziyara. Gwamnonin sun kai ziyarar ce kwana daya bayan da manyan ‘yan tawayen APC, suka Kai masa ziyara.

Gwamnonin da suka kai wa Wike ziyara, sun je ne tare da wasu tsoffin gwamnonin PDP, inda a ranar Lahadi suka gana da shi a asirce, a gidan Gwamnatin Jihar Ribas da ke Asokoro cikin garin Abuja.

Ba a san dai abin da suka tattauna ba. Amma kuma tabbas tattaunawar ba ta rasa nasaba da sabanin da ke kara tsanani tsakanin Wike da Atiku Abubakar.

Daga baya Wike ya ce Atiku ya yaudare shi, domin bayan kammala zaben, ya bi Wike har gida ya ba shi hakuri. Kuma ya ce shi zai dauka mataimakin takararsa.

Manyan PDP sun fara jin tsoron Wike tun bayan da gwamnonin APC uku daga kudu maso yamma suka kai masa ziyara.

Sai kuma ziyarar da Yakubu Dogara da Babachir Lawal suka kai masa a ranar Asabar.

Rahotanni dai da dama na nuna cewa Wike dai na cewa ba zai fita daga PDP ba, shi da jam’iyyar mutu-ka-raba.

Amma abun tambaya a nan wani irin tasiri Wike yake da shi haka har zama tamkar gwal?

Lallai wannan tambaya tana da amsa, idann aka duba irin tasirin da yake da shi a cikin harkokin siyasar Jihar Ribas da ma Nijeriya gaba daya za a ga cewa rasa irin Wike a cikin jam’iyya babban nakasu ne, domin yana da dimbin magoya baya, sannan yana iya amfani da kudinsa wajen gina jam’iyya da samun nasara a cikin siyasa.

Ya kasance wani bango da ake kallo a cikin harkokin siyasan kudancin Nijeriya da ke da tasiri wajen tsayawa kan akidarsa, wanda yake da wahalar taukwaruwa.

Tabbas Wike yana da matukar tasiri a cikin harkokin siyasar Nijeriya, musamman ma a cikin jam’iyyarsa ta PDP.

Wike
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Siyasa

Tinubu Ya Shimfiɗa Wa Arewacin Nijeriya Ayyuka Sama Da Kowane Shugaban Ƙasa – Uba Sani

July 1, 2026
Next Post
Atiku Ya Nada Dino Melaye Da Daniel Bwala A Matsayin Masu Magana da Yawunsa

2023: Wata Kungiya Zata Yi Gangamin Tara Wa Atiku Gudunmawar Biliyan 1 Na Kamfen

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.